HausaTv:
2025-06-14@13:39:52 GMT

CAN U20 : Afirka ta Kudu ta lashe kofi na farko

Published: 19th, May 2025 GMT

Tawagar ‘yan wasan kwallon kafa na ‘yan kasa da shekara 20 ta Afrika ta Kudu ta lashe kofin gasar CAN a karon farko bayan da ta doke takwararta ta Morocco (1-0) a wasan karshe da aka buga a birnin Alkahira jiya Lahadi.

Kafin hakan Najeriya ta samu matsayi na uku a gasar bayan da ta doke Masar mai masaukin baki a bugun fenariti (1-1; 4-1 a bugun fenariti).

Kasashen guda hudu da suka fafata a wasan kusa da na karshe wato (Afirka ta Kudu, Morocco, Najeriya, Masar) sun samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya na ‘yan kasa da shekaru 20 a kasar Chile da za’a gudanar daga ranar 27 ga Satumba zuwa 19 ga Oktoba, 2025.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

IPOB A Najeriya Ta Jawo Asarar Rayuka Kimani 700 Da Kuma Kudade Kimani Naira Triliyon N7.5 Tun Shekara ta 2021

Mutane kimani 776 ne suka rasa rayukansu sannan kudade kimani naira Triliyon N7.6 ne aka yi a sararsu a cikin shekaru 4 da suka gabata a yankin kudu maso gabacin Najeriya sanadiyyar zaman gida wanda kungiyar IPOB ta tilasta masu.

Jaridar Premium time ta Najeriya ta bayyana cewa rahoton hukumar tsaro na SBM Intelligence ta fitar a watan Mayon da ya gabata ya nuna cewa, da farko Kungiyar ta IPOB ta tilastawa mutanen yankin zama gida na don ganin an saki shugaban kungiyar Namdi Kano, amma daya baya sai ta zarce zuwa yanzu.

Kuma hakan ya hana abubuwan ci gaba da kuma harkokin kasuwanci makarantu da kuma ayyukan gwamnati tafiya.

IPOB dai tana bukatar warewa daga tarayyar Najeriya don kafa kasa mai suna Biafra daga yankin kudu da kuma kudu maso kudu na tarayyar Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Ranar Tattaunawa Tsakanin Wayewar Kan Kasa Da Kasa: Sabon Tunani Don Wanzar Da Zaman Lafiya Da Daidaito A Duniya
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242
  • Adadin Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Kashe A AfirkaTa Kudu Ya Karu Zuwa 49
  • Kocin Kano Pillars Usman Abdullahi Ya Ajiye Aikinsa
  • IPOB A Najeriya Ta Jawo Asarar Rayuka Kimani 700 Da Kuma Kudade Kimani Naira Triliyon N7.5 Tun Shekara ta 2021
  • An Gudanar Da Taron Ministoci Masu Daidaita Ayyukan Da Aka Amince Yayin Taron FOCAC
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa