HausaTv:
2025-05-19@10:07:19 GMT

CAN U20 : Afirka ta Kudu ta lashe kofi na farko

Published: 19th, May 2025 GMT

Tawagar ‘yan wasan kwallon kafa na ‘yan kasa da shekara 20 ta Afrika ta Kudu ta lashe kofin gasar CAN a karon farko bayan da ta doke takwararta ta Morocco (1-0) a wasan karshe da aka buga a birnin Alkahira jiya Lahadi.

Kafin hakan Najeriya ta samu matsayi na uku a gasar bayan da ta doke Masar mai masaukin baki a bugun fenariti (1-1; 4-1 a bugun fenariti).

Kasashen guda hudu da suka fafata a wasan kusa da na karshe wato (Afirka ta Kudu, Morocco, Najeriya, Masar) sun samu tikitin shiga gasar cin kofin duniya na ‘yan kasa da shekaru 20 a kasar Chile da za’a gudanar daga ranar 27 ga Satumba zuwa 19 ga Oktoba, 2025.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Cikakken Goyon Bayan Amurka Ga ‘Yan Sahayoniya Ne Yake Sa Su Tafka Laifuka

Ma’aikatar harkokin wajen Jamhuriryar musulunci ta Iran ta sanar da cewa, saboda yadda Amurka take bai wa ‘yan sahayoniya cikakken goyon baya ne, ya sa su cigaba da aikata laifuka na kisan kiyashi akan mutanen Gaza.

Bayanin da ma’aikatar harkokin wajen ta Iran ta fitar, ya zo ne  saboda tunawa da zagayowar lokacin da aka kori Falasdina aka kirkiri HKI, wanda ake kira da “Nakba” ta bayyana cewa; Falasdinawa ne suke da hakkin ayyana makomarsu,kuma nauyi ne na doka da halin kwarai akan kasashen duniya su takawa HKI birki akan kisan kiyashin da take yi a Gaza.

Bayanin ya sake jaddada kira da gabatar da masu hannu a kisan kiyashin al’ummar Gaza a gaban kotu domin su fuskanci sakamakon laifukan da su ka tafka.

Bayanin ya yi ishara da munin laifukan da ‘yan sahayoniyar suke tafkwa a Gaza, wanda ya shafi mata da kananan yara da ba su ji, ba su gani ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abin Da Ya Dace Ki Yi Yayin Haila Da Bayan Kin Gama?
  • An tafka asara bayan gobara ta ƙone Kwalejin Sheikh Dahiru Bauchi
  • Ainihin abin da ya faru da ɗan wasan Nijeriya Taiwo Awoniyi
  • Crystal Palace Ta Lashe Kofin FA Karon Farko, Ta Doke Manchester City 1-0
  • Crystal Palace ta lashe kofin FA na farko a tarihinta
  • Shuwagabanin Larabawa Sun Yi Alkawalin Sake Gina Gaza, Suna Kuma Kokarin Tsagaita Wuta Da Farko
  • Kudaden da sojojin Afirka suka kashe a bara ya karu da dala biliyan 52 a shekarar 2024
  • Iran: Cikakken Goyon Bayan Amurka Ga ‘Yan Sahayoniya Ne Yake Sa Su Tafka Laifuka
  • Gwamnatin Katsina za ta gina birnin dawakai na farko a Afirka