Wata ‘Yar Jarida Ta Nuna Mamaki Kan Nuna Damuwa Da Ciwon Biden Maimakon Kisan Gillar ‘Yan Sahayoniyya
Published: 19th, May 2025 GMT
A lokacin da kasashen Yamma suka yi biris da kisan gillar da ake yi a Gaza, kuma suna kuka kan cutar da tsohon shugaban Amurka Biden ke fama ita
Marubuciya kuma ‘yar jarida kasar Autraliya Caitlin Jahnstone a cikin wani makala da ta rubuta ta siffanta abin da ta kira matsayin munafuncin ƙasashen yamma wajen mu’amala da kimar ɗan adamtaka da gwada alhini kan batun ciwon tsohon shugaban Amurka Joe Biden game da cutar sankara da ke fama da ita a matsayin mafarin fallasa sabanin da ke cikin maganganun siyasa da kyawawan ɗabi’u na Amurka dangane da laifukan yaƙi musamman abin da ke faruwa a Gaza.
Tana cewa: Ciwon daji na Prostate yana da ‘yancin wanzuwa. Yayin da ciwon daji na Biden yana da ‘yancin kare kansa.” Johnstone ta yi izgili game da “tausayin Biden” da wasu kafofin watsa labaru na yammacin Turai da da’irori na siyasa suka nuna, tana mai sukar bacin ran da alhini da aka yi na kalamai “marasa dacewa” game da rashin lafiyar Biden, yayin da ya yi watsi da ainihin fushin dubban wadanda suka fadi sakamakon yanke shawarar siyasarsa, musamman a cikin mahallin cikakken goyon bayan Amurka ga gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila wajen aiwatar da kisan gilla kan Falasdinawa a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m
Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya kai ziyara Jihar Neja domin jajanta wa mutanen Mokwa da iftila’in ambaliyar ruwa ya shafa.
Zulum ya kuma bayar da tallafin Naira miliyan 300 domin taimaka wa waɗanda iftila’in ya shafa.
Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3Zulum, ya ce Gwamnatin Borno ta kawo wannan taimako ne don tallafabwa gwamnatin Neja wajen rage raɗaɗin ambaliyar da ta kashe mutane da lalata dukiyoyi.
Ya kuma buƙaci sauran gwamnatocin jihohi da ƙananan hukumomi su haɗa kai don kare al’umma daga iftila’i da sauyin yanayi ke haddasawa.
Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya nuna godiya bisa wannan ziyara da tallafi.
Ya ce ya yi matuƙar farin ciki da irin wannan kulawa da ƙauna da Gwamnatin Borno ta nuna wa al’ummarsa.
Bago, ya tabbatar da cewa za a yi amfani da tallafin cikin gaskiya da adalci, tare da ci gaba da faɗakar da jama’a su guji gina gidaje a kusa da bakin kogi.
Zulum, ya samu rakiyar Sanata Mohammed Tahir Monguno, wasu ‘yan Majalisar Wakilai, Injiniya Bukar Talba, Hon. Abduljadir Rahis da mataimakin kakakin Majalisar Dokokin Jihar Borno, Injiniya Abdullahi Askira.