Wata ‘Yar Jarida Ta Nuna Mamaki Kan Nuna Damuwa Da Ciwon Biden Maimakon Kisan Gillar ‘Yan Sahayoniyya
Published: 19th, May 2025 GMT
A lokacin da kasashen Yamma suka yi biris da kisan gillar da ake yi a Gaza, kuma suna kuka kan cutar da tsohon shugaban Amurka Biden ke fama ita
Marubuciya kuma ‘yar jarida kasar Autraliya Caitlin Jahnstone a cikin wani makala da ta rubuta ta siffanta abin da ta kira matsayin munafuncin ƙasashen yamma wajen mu’amala da kimar ɗan adamtaka da gwada alhini kan batun ciwon tsohon shugaban Amurka Joe Biden game da cutar sankara da ke fama da ita a matsayin mafarin fallasa sabanin da ke cikin maganganun siyasa da kyawawan ɗabi’u na Amurka dangane da laifukan yaƙi musamman abin da ke faruwa a Gaza.
Tana cewa: Ciwon daji na Prostate yana da ‘yancin wanzuwa. Yayin da ciwon daji na Biden yana da ‘yancin kare kansa.” Johnstone ta yi izgili game da “tausayin Biden” da wasu kafofin watsa labaru na yammacin Turai da da’irori na siyasa suka nuna, tana mai sukar bacin ran da alhini da aka yi na kalamai “marasa dacewa” game da rashin lafiyar Biden, yayin da ya yi watsi da ainihin fushin dubban wadanda suka fadi sakamakon yanke shawarar siyasarsa, musamman a cikin mahallin cikakken goyon bayan Amurka ga gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila wajen aiwatar da kisan gilla kan Falasdinawa a Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Gaza: hare-haren Isra’ila sun kashe mutane 100 Cikin Kwanaki Biyu
Isra’ila ta kai hare-hare da dama a safiyar Alhamis kan yankunan gabashin Khan Younis, a kudancin Zirin wanda ke nuna yadda isra’ila ke ci gaba da keta yarjejeniyar tsagaita wuta da aka cimma.
A cewar kafofin watsa labaran Falasdinawa, sama da hare-hare 10 a jere Isra’ila ta kai.
Bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna makamai masu linzami na dira akan wuraren zama a gabashin birnin.
A lokaci guda, tankunan yaki na Isra’ila da motocin sulke sun yi ruwan bama-bamai a yankunan zama a gabashin Gaza.
Sojojin Isra’ila sun kuma lalata gidaje da dama a gabashin birnin Gaza. Kasa da awa daya bayan haka, sojojin gwamnatin sun sake kai hari kan gidajen fararen hula a wannan yanki.
Hakazalika, sojojin Isra’ila na ci gaba da kai hari kan yankunan arewa maso gabashin Khan Younis, da kuma unguwannin Ma’an, Sheikh Nasser, da Joura al-Lout a kudancin birnin.
Wannan mummunan harin sama ya biyo bayan wani mummunan harin bam da ya kashe mutane sama da 109, ciki har da akalla yara 52, a fadin yankin Falasdinawa da yaki ya daidaita.
Hamas ta zargi gwamnatin Sahyoniya da karya yarjejeniyar tsagaita wuta.
Kungiyar ta yi kira ga bangaroron da suka shiga tsakani a yarjejeniyar tsagaita wutar, wato Masar, Qatar, Turkiyya da Amurka, da su dauki mataki nan take don matsa lamba ga gwamnatin isra’ila.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Sudan : Kasashen duniya na tir da cin zarafi a El-Fasher October 30, 2025 Iran Ta Jaddada Bin Hanyar Diflomasiya Ko Da A Lokacin Yaki Ne Amma Ba Zata Amince Da Bin Umarni Ba October 30, 2025 Qalibaf: Amurka Tana Yaudarar Duniya Da Zaman Lafiya, Alhalin Tana Ci Gaba Da Kai Harin Wuce Gona Da Iri October 30, 2025 Ci Gaba Da Killace Gaza Bayan Tsagaita Bude Wuta Ya Janyo Mutuwar Mutane 1000 A Yankin October 30, 2025 Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher October 30, 2025 An Kafa Dokar Ta Baci A Darul-Salam Saboda Tarzoman Zaben Shugaban Kasa A Tanzania October 30, 2025 Rasha Da Amurka Sun Sake Dawo Da Gwaje-gwajen Makaman Nukiliya October 30, 2025 Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin Faransa October 30, 2025 Sojojin HKI Sun Kutsa Kudancin Lebanon October 30, 2025 Adadin Falasdinawan Da Su Ka Yi Shahada A Cikin Sa’o’i 24 Sun Haura 100 October 30, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci