More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Ɗaya daga cikin ginshiƙan tsarin dimokuradiyya shi ne zaɓi – bai wa jama’a dama su zaɓi abin da suke so, ko kuma wanda suke so ya shugabance su.

Wannan ne ya sa ɗaya daga cikin muhimman matakai a kafuwar tsarin shi ne zaɓe.

Sai dai kuma abin tambaya shi ne, zaɓin ya haɗa har da na yin zaɓe ko ƙaurace masa?

Mene ne matsayin tsarin dimokuraɗiyya idan aka wajabta wa al’umma kaɗa ƙuri’a?

NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027? DAGA LARABA: Tasirin Mulkin Karɓa-Karɓa A Najeriya

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai duba.

Domin sauke shirin latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dimokuraɗiyya Zaɓe zaɓi

এছাড়াও পড়ুন:

Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari, Garba Shehu, ya ce sam maigidan nasa bai yi wani abu don yi wa yunƙurin Bola Tinubu na zama Shugaban Najeriya a 2023 zagon ƙasa ba.

Ya bayyana hakan ne a Abuja ranar Talata yayin wani taron manema labarai gabanin kaddamar da sabon littafin da ya rubuta a kan zamansa mai magana da yawun Buhari, wanda za a kaddamar ranar tara ga watan Yuli.

’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa

An dai yi zargin cewa da gangan Buhari ya jinkirta cire tallafin man fetur har zuwa karshen mulkinsa a 2023 domin ya hada ’yan Najeriya fada da Tinubu.

Kazalika, ’yan Najeriya sun rika sukar lamirin gwamnatin Tinubu kan kawo wahalhalu da yunwa tun bayan sanar da cire tallafin man da shugaban ya yi ranar da aka rantsar da shi.

To sai dai Garba Shehu ya karyata batun cewa an shirya cire tallafin ne saboda a yi wa Tinubu zagon kasa.

Kakakin ya ce ya cika da mamakin labarin, yana mai cewa ba yadda za a yi Buhari ya yi hakan ga dan jam’iyyarsa, tamkar daga wata jam’iyyar zai karbi mulkin daga hannunsa.

Ya ce, “Da Buhari da Tinubu duk ’yan APC ne, saboda haka ban ga ta yadda za mu shirya abin da zai yi wa gwamnatinmu zagon kasa ba.

“Buhari mutum ne da ya tsani harkar rashawa, ya shigo gwamnati da gaskiyar shi, kuma har ya gama a haka yake. Ya yi iya bakin kokarinsa ga ’yan Najeriya kuma tarihi ba zai manta da shi ba. shi ba mutum ba ne mai kwarmato, aiki kawai ya yi,” in ji Garba Shehu.

Ya kuma ce shi a karan kansa bai yi laifi ba saboda ya kyale tsohon maigidansa kuma tsohon Mataimakin Shugaban Kasa, Atiku Abubakar, ya yi aiki a gwamnatin Buhari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Isra’ila Zata Gamu Da Maida Martani Mai Tsanani Idan Ta Kuskura Ta Sabonta Yaki Da Iran
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato
  • Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu
  • DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa
  • Sabani Tsakanin Bin Gafir, Smotresh Da Zamir Kan Makomar Fursinonin Yahudawa A Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya
  •   ‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya