HausaTv:
2025-05-01@04:10:12 GMT

Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin Amurka

Published: 14th, March 2025 GMT

Iran ta yi kakkausar suka kan sabon takunkumin da Amurka ta kakabawa Ministan Man Fetur na aksar Mohsen Paknejad da wasu hukumomi da jiragen ruwa masu ruwa da tsaki a harkar danyen man fetur da kasar ke fitarwa, tana mai cewa matakin keta doka da munafunci ne daga bangaren Amurka.

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Esmaeil Baghaei ne ya bayyana hakan yau Juma’a, kwana guda bayan da ma’aikatar baitul malin Amurka ta kakaba takunkumi kan ministan man fetur na kasar Paknejad da wasu kamfanoni uku da ke da hannu a cinikin man Iran a kasar Sin.

Mista Baghaei ya ce, sabbin takunkumin sun karyata ikirarin da jami’an Amurka suke yi kan aniyarsu ta yin shawarwari tare da Iran.

Ya kara da cewa, munanan ayyukan da Amurka ta yi da nufin kawo cikas ga mu’amalar tattalin arziki da cinikayya da Iran da sauran kasashen duniya, ya zama keta dokokin kasa da kasa da cinikayya cikin ‘yanci.

Kakakin ya kara da cewa, matakin da Amurka ta dauka na na sanya wa ministan man fetur na kasar takunkumi, ba zai iya yin wani tasiri ga kudurin kasa na kare ‘yancin kai da martabar kasar da kuma kokarin samar da ci gabanta.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen

Mutane da dama daga nahiyar Afirka ne suke cikin mutane kimani 50 wadanda suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan wani gidan kaso a lardin Sa’ada na kasar Yemen.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Al-Masirah yana cewa makaman Amurka sun fada kan wani gidan yarin da aka kebewa yan Afrika, kuma yawansu ya kai 115, amma har yanzun ba’a san yawan wadanda suka rasa rayukansu a gidan yari.

Labarin ya  kara da cewa har yanzun ma’aikatan agaji suna aikin ceto a wurin, sannan hotunan da suka fara bayyana sun nuna gawaki da dama. Amma Al-Masirah ta bayyana cewa akalla mutane 68 sun rasa rayukansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araghchi : Za’ayi Tattaunawar Iran da Amurka ta gaba a Rome bayan taron E3
  • Kar A Mika Wuya Ga “Damisar Takarda”
  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Amurka ta sake laftawa wasu kamfaninin mai na Iran takunkumi
  • Ma’aikatar Sharia A Nan Iran Zata Bayyana Abinda ya farsu A Tashar Jiragen Ruwa Na Shahid Rajae
  • Riza’i: Babu Hannun  Waje A Cikin Hatsarin Da Ya Faru A Tashar Ruwa Ta Shahid Raja’i
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen