Aminiya:
2025-07-03@22:25:24 GMT

Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe

Published: 16th, June 2025 GMT

Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya umarci jami’an tsaro da su yi bincike tare da gano waɗanda suka kai hari a Jihar Benuwe, inda aka kashe sama da mutum 100.

Harin ya faru ne a ƙauyen Yelwata da ke Ƙaramar Hukumar Guma a jihar.

Iran ta rataye mutumin da ta kama yana yi wa Isra’ila leƙen asiri KADSEMA da IOM sun fara tantance ɓarnar da ambaliya ta yi a Kaduna

Bayan harin, matasa sun rufe hanyar Lafiya zuwa.

Makurdi domin nuna ɓacin ransu.

Zanga-zangar ta ci gaba da gudana har zuwa safiyar ranar Lahadi a birnin Makurdi, babban birnin jihar.

Rundunar ‘yan sandan jihar ta yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa masu zanga-zangar.

A daren ranar Lahadi, Shugaba Tinubu ya wallafa saƙo a a shafin sa na X, inda ya ce dole a kawo ƙarshen wannan kashe-kashe, kuma ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki don kama duk masu hannu a rikicin.

Tinubu ya kuma buƙaci Gwamnan Jihar Benuwe, Hyacinth Alia, da ya jagoranci tattaunawa da yin sulhu tsakanin manoma da makiyaya domin wanzar da zaman lafiya.

Ya gargaɗi shugabannin siyasa da na al’umma da su guji furucin da ka iya haifar da tarzoma.

Ya ce lokaci ya yi da za a haɗa kai domin warware matsaloli da hanyar gaskiya, adalci da fahimta, domin a samu zaman lafiya a Jihar Benuwe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: hare hare umarni

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya

Iran ta nuna makamai masu linzami wadanda suka bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya

A martanin da gwamnatin yahudawan sahayoniyya suka kai wa Iran, sojojin Iran da dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kasar sun nuna karfinsu na soji a matsayin wani bangare na “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda suka harba daruruwan makamai masu linzami na ballistic da hypersonic.

A wani bangare na wannan harin na ramuwar gayya, Iran ta kai jerin hare-hare na hadin gwiwa, wanda kaso mafi tsoka na makamai masu linzami kamar Emad, Ghadr, Fattah 1, Sejjil da Khaybar.

A halin yanzu rahotonni da hotuna daga haramtacciyar kasar Isra’ila suna kara fitowa kan yadda makamai masu linzamin Iran suka tarwatsa wurare masu muhimmanci na gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ‘yan mamaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Filato: Remi Tinubu ta ba da gudummawar Naira biliya 1
  • Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
  • Gwamnatin Yobe ta rufe kasuwanni 3 saboda matsalar tsaro
  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • Rukunin Ƴan APC A Kano Sun Nemi A Rushe Jagorancin Jam’iyyar A Jihar
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya
  • Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta
  • An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu