Kwamishiniya ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe
Published: 19th, May 2025 GMT
Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta Jihar Gombe, Asma’u Muhammad Iganus, ta ce gwamnati za ta tabbatar da an yi wa ’yar shekara biyu, Maryam Buba da ake zargin mijin mahaifiyarta, Muhammad Magaji mai shekara 47, da yi mata fyaɗe.
Kwamishiniyar tare da tawagarta sun kai ziyara gidan iyalan yarinyar da ke unguwar Jauro Innayo a Gombe, inda ta tausaya mata tare da ba su kayan tallafi kamar su pampers, sabulai da kuma kuɗi.
Asma’u ta sha alwashin cewa za a bi duk matakan shari’a domin ganin wanda ake zargi ya fuskanci hukunci.
Ta ce gwamnati na mara wa ɓangaren shari’a baya don ganin an samu adalci.
Ta jaddada ya kamata a yi wa wanda ake zargi hukuncin ɗaurin rai da rai matuƙar an same sa da laifi, domin hakan zai zama izina ga masu irin wannan ɗabi’a.
Mahaifiyar yarinyar, Hauwa’u Usman, ta gode wa Kwamishiniyar bisa goyon bayan da ta bayar da kuma addu’a a gare ta.
Ta kuma buƙaci gwamnati ta hukunta mijinta da tsauraran hukunci.
Daga bisani Kwamishiniyar, ta nufi hedikwatar ‘yan sandan Jihar Gombe don ganawa da Kwamishinan ‘yan sanda Bello Yahaya.
Sai dai ba ta same shi ba saboda yana bakin aiki.
Duk da haka, ta bar saƙo masa na gudanar da bincike tare da gurfanar da wanda ake zargi a kotu.
Muhammad Magaji, wanda ake zargi da laifin, yana hannun ’yan sanda kuma suna kan bincike.
Rundunar ’yan sandan ta tabbatar da cewa za a gurfanar da shi a kotu da zarar ta kammala bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda fyaɗe Kwamishiniya yarinya zargi wanda ake zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi
Haka kuma, wannan na faruwa ne makonni biyu bayan yin garkuwa da Pastor Friday Adehi na Christian Evangelical Fellowship of Nigeria (CEFN) tare da wani abokin cocinsa bayan kammala wa’azi. Wannan ya kara nuna yadda matsalar garkuwa ke ta’azzara a yankin Kogi East.
A gefe guda, kungiyar lauyoyi ta Najeriya (NBA), reshen Idah, ta bukaci gwamnati a matakai daban-daban da ta dauki matakan gaggawa don kawo karshen satar mutane a jihar. Shugaban kungiyar, Barr. James Michael, ya ce yawaitar garkuwa a kan titunan yankin ya jefa rayukan jama’a cikin hatsari, don haka gwamnati ya kamata ta dauki tsauraran matakai domin kare lafiyar al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp