Kwamishiniya ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe
Published: 19th, May 2025 GMT
Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta Jihar Gombe, Asma’u Muhammad Iganus, ta ce gwamnati za ta tabbatar da an yi wa ’yar shekara biyu, Maryam Buba da ake zargin mijin mahaifiyarta, Muhammad Magaji mai shekara 47, da yi mata fyaɗe.
Kwamishiniyar tare da tawagarta sun kai ziyara gidan iyalan yarinyar da ke unguwar Jauro Innayo a Gombe, inda ta tausaya mata tare da ba su kayan tallafi kamar su pampers, sabulai da kuma kuɗi.
Asma’u ta sha alwashin cewa za a bi duk matakan shari’a domin ganin wanda ake zargi ya fuskanci hukunci.
Ta ce gwamnati na mara wa ɓangaren shari’a baya don ganin an samu adalci.
Ta jaddada ya kamata a yi wa wanda ake zargi hukuncin ɗaurin rai da rai matuƙar an same sa da laifi, domin hakan zai zama izina ga masu irin wannan ɗabi’a.
Mahaifiyar yarinyar, Hauwa’u Usman, ta gode wa Kwamishiniyar bisa goyon bayan da ta bayar da kuma addu’a a gare ta.
Ta kuma buƙaci gwamnati ta hukunta mijinta da tsauraran hukunci.
Daga bisani Kwamishiniyar, ta nufi hedikwatar ‘yan sandan Jihar Gombe don ganawa da Kwamishinan ‘yan sanda Bello Yahaya.
Sai dai ba ta same shi ba saboda yana bakin aiki.
Duk da haka, ta bar saƙo masa na gudanar da bincike tare da gurfanar da wanda ake zargi a kotu.
Muhammad Magaji, wanda ake zargi da laifin, yana hannun ’yan sanda kuma suna kan bincike.
Rundunar ’yan sandan ta tabbatar da cewa za a gurfanar da shi a kotu da zarar ta kammala bincike.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda fyaɗe Kwamishiniya yarinya zargi wanda ake zargi
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
Daga Usman Muhammad Zaria
Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta yi kira ga mazauna jihar Jigawa da su kasance masu bin doka da oda, tare da yin aiki kafada da kafada da rundunar ‘yan sanda domin tabbatar da tsaro da kwanciyar hankali a fadin jihar.
Kwamishinan ‘Yan Sanda na jihar Jigawa, CP Dahiru Muhammad, ne ya bayyana haka lokacin da ya karɓi sabbin motoci 10 kirar Toyota Hilux da Gwamna Umar Namadi ya bai wa rundunar a Dutse, babban birnin jihar.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar, SP Lawan Shiisu Adam, ya fitar, CP Dahiru Muhammad ya yaba da jajircewar Gwamna Umar Namadi wajen tallafa wa hukumomin tsaro domin sauke nauyin da ke kansu a jihar.
Ya bayyana cewa, wannan gudummawa ta nuna cikakken kudirin gwamnatin Gwamna Namadi na ƙara inganta harkokin tsaro da kuma tallafawa Rundunar ‘Yan Sanda ta Najeriya wajen aiwatar da aikinta na kare rayuka da dukiyoyin jama’a a fadin jihar.
Kwamishinan ya nuna cewa, waɗannan sabbin motoci 10 za su taimaka matuƙa wajen rage lokacin da ake ɗauka kafin amsa kiran gaggawa, tare da ƙara inganta aikin rundunar a fadin jihar.
Ya ƙara da cewa, za a yi amfani da motocin yadda ya kamata, tare da kula da su don tabbatar da ingantaccen tsaro.
CP Dahiru Muhammad ya kuma sake jaddada aniyar rundunar wajen ci gaba da tabbatar da zaman lafiya, doka da oda, tare da ƙarfafa haɗin gwiwa da sauran hukumomin tsaro da masu ruwa da tsaki.