Aminiya:
2025-06-15@18:45:38 GMT

Zulum ya bai wa jami’an tsaro kyautar gidaje da motoci a Borno

Published: 15th, March 2025 GMT

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya bai wa jami’an ‘yan sanda kyautar gidaje 280 tare da bayar da gudunmuwar motoci 110 da babura 500 domin inganta tsaro a jihar.

Wannan shiri na da nufin inganta jin daɗin jami’an tsaro da kuma ƙarfafa yaƙi da aikata laifuka da ta’addanci.

MC Tagwaye ya fice daga APC zuwa SDP ’Yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Kaduna, sun sace matasa 3

A wajen bikin rabon kayayyakin a Maiduguri, Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, ya jinjina wa gwamna Zulum kan goyon bayansa ga jami’an tsaro.

Ya ce wannan tallafi mataki ne mai kyau wajen tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Borno.

“Ba za mu yi ƙasa a gwiwa ba wajen kula da jin daɗin jami’an da ke sadaukar da rayuwarsu don kare al’umma,” in ji Zulum.

“Waɗannan motoci za su taimaka wajen inganta zirga-zirga da hanzarta kai ɗauki a lokacin buƙata.”

Egbetokun ya bayyana wannan gudunmuwa a matsayin wani babban ci gaba.

“Wannan tallafi zai ƙarfafa gwiwa da inganta ayyukan jami’anmu,” in ji shi.

Gwamnan ya kuma gode wa Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, bisa jagorancinsa wajen tallafa wa jami’an tsaro.

Ya tabbatar da cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da samar da kayan aiki da duk wani abu da zai taimaka wajen tabbatar da tsaro a jihar.

Manyan jami’an tsaro, ciki har da shugabannin ’yan sanda da sojoji, sun halarci taron, inda suka jaddada buƙatar haɗin gwiwa don tunkarar ƙalubalen tsaro a jihar.

Ga hotunan a ƙasa:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Jami an Tsaro kyauta jami an tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Himmatu Wajen Inganta Karfin Sashen Fetur Da Gas Na Cikin Gida
  • Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran