Aminiya:
2025-05-19@18:35:06 GMT

Mawaƙan APC sun zargi gwamnatin Jigawa da yin watsi da su

Published: 19th, May 2025 GMT

Wasu mawaƙan jam’iyyar APC da ke Jihar Jigawa, sun bayyana ɓacin ransu kan yadda gwamnatin jihar ta yi watsi da su, duk da irin gudunmawar da suka bayar wajen samun nasarar jam’iyyar a zaɓen 2023.

Mawaƙan wajen su 35, sun gudanar da wani taro, inda suka bayyana damuwarsu da kuma sanar da cewa sun janye daga duk wata hulɗa da gwamnatin jihar, har sai an ba su kulawar da ta dace.

Hajji: Gwamnan Gombe ya yi bankwana da maniyyata 966, ya bai wa kowa kyautar Riyal 200 NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?

Shugaban mawaƙan jihar, Lawan Gujungu Mai Babban Gandu ne, ya jagoranci taron, inda ya shaida wa manema labarai cewa tun bayan da sabon gwamnan ya hau mulki sama shekara biyu, har yanzu ba su sharɓi romon dimokuraɗiyya ba.

Ya ce mawaƙan sun yi haƙuri na tsawon lokaci suna sa ran za a saka musu, amma abin ya gagara.

A cewarsa: “Mun shiga mawuyacin hali. Muna cikin APC tun asali, mun yi wa jam’iyya hidima sosai a lokacin yaƙin neman zaɓe, mun ƙirƙiri waƙoƙi da dama don tallata manufofin jam’iyyar da kwatanta cancantar ’yan takararta.

“Amma yanzu da muka ci zaɓe kuma muka kafa gwamnati, an watsar da mu tamkar ba mu da wata ƙima.”

Lawan, ya ƙara da cewa daga yanzu mawaƙan za su nisanci duk wani taro ko aikin da ya shafi gwamnati, har sai an saurare su tare da mutunta su da irin gudunmawar da suka bayar.

Wannan bore ya fito fili ne a daidai lokacin da ake buƙatar jituwa da haɗin kai tsakanin masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar da kuma gwamnatin jihar domin ci gaban al’umma.

Wasu daga cikin mawaƙan da suka halarci taron sun bayyana cewa suna fatan gwamnan zai ji ƙorafinsu kuma ya ɗauki matakin da ya dace, domin ci gaba da gina jam’iyya da gwamnatin da kowa ke alfahari da ita.

Tuni dai wannan batu ya jawo ce-ce-ku-ce a cikin jam’iyyar APC a Jihar Jigawa, inda wasu ke ganin cewa ya kamata gwamnati ta sake duba rawar da waɗanda suka ba da gudunmawa kafin kafa gwamnati, domin gudun fuskantar tawaye.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati Jigawa Ƙorafu Mawaƙa taro

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su

Gwamnan jihar Kwara AbdulRahman AbdulRazaq ya aika ta’aziyya ga iyalan mutane 37 da hatsarin kwale-kwalen Gbajibo ya rutsa da su daga jihar Neja a karshen mako.

 

A cikin sanarwar gwamna AbdulRazaq ya jajantawa gwamnati da al’ummar jihar Neja kan wannan lamari mai ban tausayi.

 

Gwamnan ya bukaci ma’aikatan jirgin da fasinjoji da su bi ka’idojin tsaro domin amfanin kowa.

 

Ya bayyana a matsayin al’ada mai raɗaɗi kuma ba za a yarda da ita ta rashin amfani da na’urorin kariya da gwamnati ta bayar akai-akai.

 

Yana rokon Allah ya jikan wadanda aka kashe.

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mawaƙan APC sun zargi gwamnati da watsi da su a Jigawa
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su
  • APC Ta Zargi Gwamnan Zamfara Da Shirga Karya Tare Da Kiran Ya Nemi Afuwar Zamfarawa
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi
  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta
  • Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?
  • Tawagar NAHCON Ta Kai Ziyarar Gani Da Ido Jihar Jigawa
  • Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jihar Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu