Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-05-19@17:03:20 GMT

Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.

Published: 19th, May 2025 GMT

Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.

Mutane 7 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu goma sha daya suka samu munanan raunuka a wani hatsarin mota da ya afku a unguwar Essa dake kan titin Agaie Badeggi a karamar hukumar Katcha a jihar Neja.

 

Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, NSEMA Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar hatsarin a wata sanarwa da ta raba wa manema labarai a Minna.

 

A cewar Abdullahi Baba Arah, motar na dauke da hatsin gwamnatin tarayya, da kuma wata mota dake dauke da wasu fasinjoji 36, wadanda dukkansu maza ne zasu jihar Kano daga jihar Legas suka yi toho mu gama a lokacin da hatsarin ya afku.

 

Hatsarin ya afku ne da misalin karfe uku na safiyar yau, sakamakon rashin kyawun hanya a layin Lambata, Bida.

 

Ya zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, an tabbatar da mutuwar mutane 7,  11 da suka samu munanan raunuka, yayin da mutane 5 suka samu kananan yara.

 

Wasu daga cikin wadanda suka jikkata an kai su cibiyoyin lafiya na Badeggi da Agaie, wasu kuma abokan aikinsu sun tafi da su yayin da ‘yan uwansu kuma suka tafi da wadanda suka mutu domin yi musu jana’iza.

 

A halin da ake ciki dai hukumar NSEMA ta gudanar da aikin bincike da ceto tare da matafiya da wasu mutanen kauyen da ke kusa da inda lamarin ya faru.

 

PR ALIYU LAWAL

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hadari

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh                                                                                                              

An zartar da hukuncin kisa a kan wasu mutane 3 da ake zargi da kai harin ta’addanci a hubbaren Shah Cheragh

Shugaban hukumar shari’a ta lardin Fars (a kudancin Iran) ya sanar da cewa: Kotun Musulunci a birnin Shiraz ta yanke hukunci kan wasu mutane 7 da ake tuhuma da hannu a harin ta’addancin da aka kai a hubbaren Shah Cheragh (Ahmad ibn Imam Musa al-Kazim, amincin Allah ya tabbata a gare shi).

Haka nan kuma yayin da yake ishara da hukuncin da aka yanke wa mutanen bakwai da suka kai harin ta’addanci a hubbaren Shahragh, Hujjat al-Islam Sayyid Sadrullah Raja’i Nasab ya ce: A cikin hare-haren ta’addancin da aka kai a hubbaren Shahragh, baya ga manyan wadanda suka kai harin da aka hukunta bisa ayyukansu; An kuma hukunta wasu mutane saboda goyon baya da kuma tarayya da suka wajen samar da makamai da alburusai. Sannan bisa taimakon matakan leken asirin da aka sanya a cikin ajandar mai bincike na musamman da jami’an tsaro bayan faruwan wadannan al’amura, an gano wadannan mutane, an kama su, kuma sannan an dakile shirinsu na ta’addanci.

Hukunce-hukuncen sun hada da hukuncin kisa ga wasu mutane uku da aka samu da laifin “taimakawa wajen yada barna a kan doron kasa,” kuma an bayyana wadanda ake tuhumar a matsayin “masu kitsa” ayyukan ta’addanci. An kuma yanke musu hukuncin daurin shekaru 25 a kan kowane wanda ake tuhuma bisa zargin “taimakawa wajen gudanar da barna.”

An yanke wa wani dan ISIS hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari, wani kuma shekaru 10 da kwana daya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
  • Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh                                                                                                              
  • Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno
  • Mutum 3 sun mutu, 21 sun jikkata a turmutsitsin karɓar kuɗin tallafi a Borno
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • Fiye Da Falasdinawa 300 Ne Su Ka Yi Shahada Da Jikkata Daga Safiyar Yau Juma’a