Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.
Published: 19th, May 2025 GMT
Mutane 7 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu goma sha daya suka samu munanan raunuka a wani hatsarin mota da ya afku a unguwar Essa dake kan titin Agaie Badeggi a karamar hukumar Katcha a jihar Neja.
Darakta Janar na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja, NSEMA Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar hatsarin a wata sanarwa da ta raba wa manema labarai a Minna.
A cewar Abdullahi Baba Arah, motar na dauke da hatsin gwamnatin tarayya, da kuma wata mota dake dauke da wasu fasinjoji 36, wadanda dukkansu maza ne zasu jihar Kano daga jihar Legas suka yi toho mu gama a lokacin da hatsarin ya afku.
Hatsarin ya afku ne da misalin karfe uku na safiyar yau, sakamakon rashin kyawun hanya a layin Lambata, Bida.
Ya zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, an tabbatar da mutuwar mutane 7, 11 da suka samu munanan raunuka, yayin da mutane 5 suka samu kananan yara.
Wasu daga cikin wadanda suka jikkata an kai su cibiyoyin lafiya na Badeggi da Agaie, wasu kuma abokan aikinsu sun tafi da su yayin da ‘yan uwansu kuma suka tafi da wadanda suka mutu domin yi musu jana’iza.
A halin da ake ciki dai hukumar NSEMA ta gudanar da aikin bincike da ceto tare da matafiya da wasu mutanen kauyen da ke kusa da inda lamarin ya faru.
PR ALIYU LAWAL
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hadari
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda mota ta kashe mutum 8 ’yan gida daya bayan dawowa daga yawon Sallah a Kaduna
Wani mummunan hatsarin mota a hanyar Kaduna zuwa Zariya ya yi sanadin mutuwar mutum takwas ’yan gida daya, yayin da wasu mutum biyu ke can kwance a asibiti rai a hannun Allah.
Rahotanni sun ce lamarin ya faru ne wajen misalin karfe 6:00 na yammacin ranar Litinin a garin Barakallahu da ke kan hanyar Kaduna zuwa Zariya, ana tsaka da bukukuwan Babbar Sallah.
A cewar rahotannin, lamarin ya faru ne lokacin da wata mota da ke tsala gudu ta kwace sannan ta danne mutanen da ke tsaye a gefen hanya bayan dawowarsu daga yawon sallah.
Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin IndiaA cewar mahaifin mamatan, Malam Jamilu Usman Maiyadi, wata mota kirar GLK Marsandi mai ruwan toka ce ta take iyalan nasa, kuma wani yaro ne yake tuka ta.
Sai da a cewarsa, yaron wanda suka yi ittifakin dan gidan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin, ya cika wandonsa da iska bayan faruwar lamarin.
Ya ce, “Mun rasa iyalai takwas ’yan gida daya a rana daya. Daga ciki akwai matata Khadija Umar da ’ya’yana su biyu sai kuma kanne da yayyen matar tawa da kuma wata gwaggonsu, duk sun mutu.
“A jimlance, mutum takwas kenan motar ta take; takwas sun mutu nan take, biyu kuma har yanzu suna asibiti,” in ji shi.
Malam Jamilu ya ce iyalan nasa na tsaye ne a bakin hanya suna jiran su sami motar da za ta kai su gida lokacin da motar ta kwace daga kan titi ta afka musu.
Ya kuma ce, “Tabbas motar na gudun wuce sa’a lokacin faruwar lamarin saboda kafar matata ta yi karayar da ba za a iya gyarawa ba, sannan sai jami’an hukumar kiyaye hadura ne ma daga baya suka gano wasu sassan jikin dana Sadiq,” Malam Jamilu ya fada fuskarsa cike da alhini.
‘Har da mai cikin wata takwas da za ta haifi tagwaye a cikin wadanda suka mutu’
Daga cikin wadanda suka rasu har da Zainab Muhammad wacce ke dauke da juna-biyun wata takwas da za ta haifi tagwaye.
Mijin marigayiyar, Sulaiman Abdulkadir Mai Shinkafa, wanda malamin addini ne a Hayin Rigasa, ya bayyana lamarin a cikin alhini.
Ya ce, “Ta kusa haihuwa. Mun riga mun sayi duk kayan jarirai muna shirye-shiryen haihuwar. Har mun ma sanya wa jariran sunan Hassan da Hussaini. Sannan akwai danmu mai shekara shida mai suna Khalid da aka kashe.
“An take matar tawa, sannan dana sai da muka kankaro namansa da katako kafin a yi musu jana’iza. Abu ne da babu wanda zai yi fatan ya gani a rayuwarsa.”
‘Ko uffan iyalan yaron da ya take mu ba su ce mana ba’
Kamar sauran masu alhinin, Malam Sulaiman ya nuna takaici kan yadda ya ce iyalan yaron da gwamnati sun yi watsi da su ko uffan ba su ce musu ba.
“Babu wani daga cikin iyalan yaron, wanda dan wani fitaccen dan siyasa ne a yankin da ya tuka motar, ko kuma daga gwamnatin jihar Kaduna da ya zo ya yi mana ta’aziyya.
“Ko uffan ba su ce mana ba. hatta mahaifin direban motar bai zo ba, sai ka ce yaruwar iyalan namu ba ta da wani amfani,” in ji shi.
Hukumar Kiyaye Hadura ta Kasa (FRSC) ta tabbatar da faruwar lamarin inda ta alakanta shi da gudun wuce sa’a da kuma kwacewar mota a kan hanyar da ba a jima da dauke ruwan sama ba.
Kwamandan shiyya na hukumar a Kaduna, Tijjani Iliyasu ne ya tabbatar da hakan.
Sai dai ya ce sun mika lamarin zuwa hannun ’yan sanda domin fadada bincike a kai.
Kazalika, duk kokarin wakilinmu na jin ta bakin rundunar ’yan sandan Kaduna da gwamnatin jihar sun ci tura saboda sun ki cewa komai a kai.