Cututtukan Da Ba Sa Yaduwa Sun Kai Kashi 30% Na Mace-Mace A Najeriya – Cappa
Published: 19th, May 2025 GMT
An gano cututtukan da ba sa yaduwa (NCDs) a matsayin manyan abubuwan da ke haifar da mutuwa a Najeriya, wanda ya kai kusan kashi 30% na yawan mace-macen da ake samu a kasar.
Babban daraktan kula da harkokin kasuwanci da hada-hadar jama’a na Afirka (CAPPA) Akinbode Oluwafemi ya bayyana haka a lokacin wani horon aikin jarida kan sa ido kan haraji da masana’antu na Sugar-Sweetened (SSB) da aka gudanar a Kano.
Ya kara da cewa a halin yanzu Najeriya na fuskantar matsalar rashin lafiyar al’umma da dabi’ar abinci ke haifarwa, musamman yawan cin abinci da aka sarrafa sosai kamar abubuwan sha masu zaki da sikari da sinadarin sodium.
“Kamfanonin abinci suna amfani da dabarun tallata na zamani don jawo hankalin ‘yan Najeriya musamman yara da matasa su cinye wadannan kayayyakin marasa lafiya,” in ji shi.
“Wannan ba wai kawai yana illa ga lafiyar mutum bane amma yana hannu riga da manufofin kiwon lafiyar jama’a da kuma nauyi tsarin kiwon lafiya.”
Ya yi nuni da cewa, domin magance hakan, gwamnatin Najeriya ta bullo da harajin shaye-shaye kayan zaki (SSB) a shekarar 2021, wanda ke sanya harajin ₦10 a kowace lita kan duk wani abin sha da ba na barasa ba, da zaki da kuma carbonated.
“Manufar tana da nufin hana yawan shan abubuwan sha mai zaki, rage dogaro da irin wadannan abubuwan sha, da kuma dakile hauhawar cututtukan da ba su da alaka da SSB.”
Ya ce horon da aka yi a Kano, an yi shi ne da nufin karfafawa ’yan jarida kwarin guiwa wajen bayar da rahotanni daidai kan al’amuran da suka shafi kiwon lafiyar jama’a, musamman cututtuka da ba sa yaduwa da kuma tasirin manufofin da suka shafi kiwon lafiya.
A cikin sakonnin fatan alheri, mataimakin daraktan l, abubuwan haɗari, ma’aikacin ma’aikatar lafiya ta tarayya Dr. Dorothy Amadi da Joy Amafah daga Global Health Advocacy incubator (GHAI) sun bayyana horon da ya dace.
Sun bayyana kafafen yada labarai a matsayin masu ruwa da tsaki kuma sun bukace su da su yi amfani da dandamalin su don bayar da rahoton abubuwan da suka shafi lafiya.
Khadija Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Lafiya kiwon lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya mayar wa da Shugaban Amurka, Donald Trump martani cewa Najeriya ba ta yadda da duk wani nau’in zarafin addini.
Tinubu, ya yi wannan bayani ne bayan Trump ya sake sanya Najeriya cikin jerin ƙasashen da ake kiran “Ƙasashen da ke da Babbar Matsala wajen ’Yancin Addini.”
PDP ta dakatar da Anyanwu da wasu ’yan tsagin Wike Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura IsaTrump ya yi iƙirarin cewa Kiristoci a Najeriya na fuskantar barazana, amma ya sha alwashin cewa Amurka za ta kare su.
A cikin wani saƙo da ya wallafa a kafafen sada zumunta, Trump ya rubuta cewa: “Addinin Kirista yana fuskantar babbar barazana a Najeriya. Ana kashe dubban Kiristoci.”
A ranar Asabar, Tinubu ya mayar da martani ta kafar sada zumunta, inda ya ce Najeriya ƙasa ce mai dimokuraɗiyya wadda kundinta ya tabbatar da ’yancin yin addini.
“Najeriya tana da cikakken tanadi a kundinta da ya tabbatar da ’yancin yin addini,” in ji Tinubu.
“Tun daga shekarar 2023, gwamnatina na aiki tare da shugabannin Kiristoci da Musulmai don magance matsalolin tsaro da ke shafar jama’a daga kowane ɓangare da addini.”
Ya ƙara da cewa, kiran Najeriya ƙasa mai matsala wajen gudanar addini ba gaskiya ba ne.
“Za mu ci gaba da kare ’yancin kowane ɗan ƙasa na yin addininsa cikin walwala. Najeriya ba ta goyon bayan zaluncin addini ko kaɗan,” in ji Tinubu.
Ya kuma ce Najeriya za ta ci gaba da haɗa kai da Amurka da sauran ƙasashe domin inganta zaman lafiya da fahimtar juna tsakanin mabiya addinai daban-daban.