An gano cututtukan da ba sa yaduwa (NCDs) a matsayin manyan abubuwan da ke haifar da mutuwa a Najeriya, wanda ya kai kusan kashi 30% na yawan mace-macen da ake samu a kasar.

 

 

Babban daraktan kula da harkokin kasuwanci da hada-hadar jama’a na Afirka (CAPPA) Akinbode Oluwafemi ya bayyana haka a lokacin wani horon aikin jarida kan sa ido kan haraji da masana’antu na Sugar-Sweetened (SSB) da aka gudanar a Kano.

 

 

Ya kara da cewa a halin yanzu Najeriya na fuskantar matsalar rashin lafiyar al’umma da dabi’ar abinci ke haifarwa, musamman yawan cin abinci da aka sarrafa sosai kamar abubuwan sha masu zaki da sikari da sinadarin sodium.

 

 

“Kamfanonin abinci suna amfani da dabarun tallata na zamani don jawo hankalin ‘yan Najeriya musamman yara da matasa su cinye wadannan kayayyakin marasa lafiya,” in ji shi.

 

 

“Wannan ba wai kawai yana illa ga lafiyar mutum bane amma yana hannu riga da manufofin kiwon lafiyar jama’a da kuma nauyi tsarin kiwon lafiya.”

 

 

Ya yi nuni da cewa, domin magance hakan, gwamnatin Najeriya ta bullo da harajin shaye-shaye kayan zaki (SSB) a shekarar 2021, wanda ke sanya harajin ₦10 a kowace lita kan duk wani abin sha da ba na barasa ba, da zaki da kuma carbonated.

 

 

“Manufar tana da nufin hana yawan shan abubuwan sha mai zaki, rage dogaro da irin wadannan abubuwan sha, da kuma dakile hauhawar cututtukan da ba su da alaka da SSB.”

 

 

Ya ce horon da aka yi a Kano, an yi shi ne da nufin karfafawa ’yan jarida kwarin guiwa wajen bayar da rahotanni daidai kan al’amuran da suka shafi kiwon lafiyar jama’a, musamman cututtuka da ba sa yaduwa da kuma tasirin manufofin da suka shafi kiwon lafiya.

 

 

A cikin sakonnin fatan alheri, mataimakin daraktan l, abubuwan haɗari, ma’aikacin ma’aikatar lafiya ta tarayya Dr. Dorothy Amadi da Joy Amafah daga Global Health Advocacy incubator (GHAI) sun bayyana horon da ya dace.

 

 

Sun bayyana kafafen yada labarai a matsayin masu ruwa da tsaki kuma sun bukace su da su yi amfani da dandamalin su don bayar da rahoton abubuwan da suka shafi lafiya.

 

Khadija Aliyu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Lafiya kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos

Babbar Kotun Jihar Filato da ke zamanta a Jos, ta yanke wa dalibin nan na makarantar GSTC Bukuru, Odey Emmanuel, hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda kashe malamin makarantarsu a kan abinci.

Alkalin kotun, Mai Shari’a S.J. Bakfur, ya ce an sami Odey ne da laifin na kisan kai wanda kotun ta ce ya saba da tanade-tanaden sassa na 188 na 189 na kundin dokar manyan laifuffuka ta jihar Filato ta shekara ta 2017.

Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta Ko ɗaya Buhari bai yi wa takarar Tinubu zagon ƙasa ba – Garba Shehu

A cewar alkalin, masu shigar da kara sun gabatar da hujjojin da suka iya gamsar da kotun cewa wanda ake zargin ya aikata laifin da aka zarge shi da aikatawa.

Babban lauyan gwamnatin jihar kuma Kwamishinan Shari’a, Philemon Audu Daffi ne ya jagoranci lauyoyi masu gabatar da kara.

Lamarin dai ya faru ne ranar 30 ga watan Yulin 2022, a cikin harabar makarantar da ke karamar hukumar Jos ta Kudu.

Lauyoyin sun shaida wa kotun cewa dalibin ya kasha malamin ne mai suna Job Dashe a dakin girkin makarantyar lokacin da ake rabon abinci ga dalibai.

Sun ce a lokacin ne malamin a hukunta dalibin bisa zargin ya karbi kason abinci har sau biyu, inda dalibai suka tabbatar da haka, lamarin da ya harzuka dalibin.

Daga nan ne dalibin ya dauko wuka ya daba wa malamin a kahon zuciya, nan take aka garzaya da shi asibiti amma kafin a je y ace ga garinku nan.

Sai dai ko da a aka karanta masa laifin da aka zarge shi da aikatawa a kotun, dalibin bai musa ba.

Da yake yanke hukuncin, Alkalin kotun ya jaddada cewa kisan malami a makaranta babbar barazana ce ga al’umma da ya zama wajibi a dauki tsattsauran mataki a kai.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13
  • Buhari Ba Shi Da Lafiya, Amma Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
  • Buhari Ba Shi Da Lafiya, Yana Samun Sauƙi A Birtaniya — Garba Shehu
  • NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta
  • An Hori Ma’aikatan Lafiya Su Kara Kokari Wajen Rike Aikin su
  • Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
  • Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata guda bayan ambaliya
  •   ‘Yan Guudun Hijirar Sudan Miliyan 4 Suna Fuskantar Yunwa A Kasashen Makwabta
  • NAJERIYA A YAU: Halin da al’ummar Mokwa ke ciki wata 2 bayan ambaliya