Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da nuna wasu manyan fina-finai masu dogon zango 22 sakamakon zarginsu da saɓa ƙa’idar hukumar.

 

Cikin wata sanarwa da jami’in hul da jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar ya ce shugaban hukumar Abba Al-Mustapha ne bayar da umarcin saboda a cewarsa masu shirya fina-finan sun saɓa ƙa’idojin hukumar waɗanda suka tanadi cewa dole ne hukumar ta tace su kafin fitar da su.

 

Wasu daga cikin fina-finan da dakatarwa ta shafa sun haɗa da

 

Dadin Kowa

Labarina

Gidan Sarauta

Manyan Mata

Dakin Amarya

Kishiyata

Garwashi

Jamilun Jiddan

Mashahuri

Wasiyya

Tawakkaltu

Mijina

Wani Zamani

Mallaka

Kudin Ruwa

Boka Ko Malam

Wayasan Gobe

Rana Dubu

Fatake

Shahadar Nabila

Tabarmar

Rigar Aro

An umurci masu shirya fina-finan da abin ya shafa da su dakatar da duk wani nau’i na watsa shirye-shirye ko yawo nan da nan tare da gabatar da abubuwan da ke cikin su don amincewar tantancewa a cikin mako guda daga Litinin, Mayu 19 zuwa Litinin, Mayu 26, 2025.

Hukumar ta kuma yi kira ga gidajen Talabijin da Hukumar Yada Labarai ta Najeriya (NBC) da su taimaka wajen tabbatar da wadannan ka’idoji, tare da yin daidai da kokarin inganta kwarewa da bunkasar masana’antar Kannywood.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar KNARDA Ta Ƙudiri Aniyar Yashe Madatsun Ruwa A Kano 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukuma Ta Dakatar Da Haska Fina-Finai 22 Har Sai Baba Tagani
  • Gwamnatin Kano ta dakatar da haska shirin Labarina da Dadin Kowa da wasu 20
  • Kafofin Yada Labarai Na Amurka Sun Bayyana Kuzari Da Ci Gaban Da Fina-finan Kasar Sin Ke Samu A Bikin Cannes 
  • Zargin Kin Amincewar Kwankwaso Zuwa APC: Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Mai Taimaka Ma Ta
  • Abba ya dakatar da hadiminsa saboda furta kalamai a kan Kwankwaso
  • Hukumar KNARDA Ta Ƙudiri Aniyar Yashe Madatsun Ruwa A Kano 
  • Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta
  • Max Air Zai Yi Jigilar Alhazan Jihar Jigawa A Ranakun 20 Da 21 Ga Watan Mayu
  • CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU