Gwamnatin Kano Ta Dakatar Da Nuna Wasu Manyan Fina-Finai 22
Published: 19th, May 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da nuna wasu manyan fina-finai masu dogon zango 22 sakamakon zarginsu da saɓa ƙa’idar hukumar.
Cikin wata sanarwa da jami’in hul da jama’a na hukumar, Abdullahi Sani Sulaiman ya fitar ya ce shugaban hukumar Abba Al-Mustapha ne bayar da umarcin saboda a cewarsa masu shirya fina-finan sun saɓa ƙa’idojin hukumar waɗanda suka tanadi cewa dole ne hukumar ta tace su kafin fitar da su.
Wasu daga cikin fina-finan da dakatarwa ta shafa sun haɗa da
Dadin Kowa
Labarina
Gidan Sarauta
Manyan Mata
Dakin Amarya
Kishiyata
Garwashi
Jamilun Jiddan
Mashahuri
Wasiyya
Tawakkaltu
Mijina
Wani Zamani
Mallaka
Kudin Ruwa
Boka Ko Malam
Wayasan Gobe
Rana Dubu
Fatake
Shahadar Nabila
Tabarmar
Rigar Aro
An umurci masu shirya fina-finan da abin ya shafa da su dakatar da duk wani nau’i na watsa shirye-shirye ko yawo nan da nan tare da gabatar da abubuwan da ke cikin su don amincewar tantancewa a cikin mako guda daga Litinin, Mayu 19 zuwa Litinin, Mayu 26, 2025.
Hukumar ta kuma yi kira ga gidajen Talabijin da Hukumar Yada Labarai ta Najeriya (NBC) da su taimaka wajen tabbatar da wadannan ka’idoji, tare da yin daidai da kokarin inganta kwarewa da bunkasar masana’antar Kannywood.
KHADIJAH ALIYU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Ce Babu Batun Tattaunawa Duk Tare Da Amurkawa Sun Ce Za’a Yi
Kakakin gwamnatin JMI ta bayyana cewa a dai-dai lokacinda Amurka ta kai hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliyar kasar , babu wata tattaunawa da Amurka nan kusa, duk tare da cewa Amurkawan sun bayyana cewa za’a ci gaba da shi.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kakakin gwamnatin kasar Iran Malama Fatimah Muhajirani tana fadar haka a jiya Talata, ta kuma kara da cewa, babu wata rana da aka sanya na tattaunawa da Amurka kuma mai yuwa babu wata tattaunawa da ita nan kusa.
Fatima tana maida martani ne ga wata sanarwan da gwamnatin kasar Amurka ta bayara na, na cewa nan kusa zasu sake farfado da tattaunawa da JMI. Tehran dai ta bayyana cewa bata bukatar wani tattaunawa da Amurka kuma bayan hare-haren da ta kai kan cibiyoyin nukliyar kasar guda 3 a dai dai lokacinda HKI ta fadawa kasar da yaki tare da amincewarta.