Dare da aka zubar da jini mafi muni a Gaza: Sama da Falasdinawa 80 ne suka yi shahada a sassa daban-daban na Zirin

Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan fararen hula a yankuna daban-daban na zirin Gaza, inda suka yi sanadiyyar shahadan sama da Falasdinawa 80, kuma mafi yawansu a wani kisan kiyashi da aka yi wa ‘yan gudun hijira a yankin Al-Mawasi na Khan Yunus da ke kudancin zirin Gaza, bayan da aka jefa bama-bamai da kona tantunansu a kusa da Asibitin kwararru na Kuwait, baya ga kisan kiyashi a duk fadin yankin.

Majiyoyin Falasdinawa sun ce an kona mutane 36, yawancinsu mata da kananan yara, bayan da sojojin mamayar Isra’ila suka yi ruwan bama-bamai a tantunansu, tare da cinna musu wuta. An kuma kai harin bama-bamai a gidaje hudu a yankin Abasan da biyu a Al-Fakhari.

Har ila yau sojojin mamayar sun kai hare-haren bama-bamai a wasu gidaje a tsakiyar zirin Gaza, inda suka kashe mutane 9 a Az-Zawayda da 3 a Deir al-Balah.

A arewacin Zirin Gaza, jiragen sama sojin mamayar sun kai hari kan gidajen fararen hula, inda suka kashe Falasdinawa 12 a gidan Nasser Jabalia al-Nazla, 8 a wani gida a Jabaliya al-Balad, da shahidai 7 a gidan al-Barawi a garin Beit Lahiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu da wasu mutum 4 a Sakkwato

Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kashe mutum biyar, ciki har da wata mata mai juna biyu a ƙauyen Alkalije da ke Ƙaramar Hukumar Yabo ta Jihar Sakkwato.

Lamarin ya faru ne da sanyin safiyar Litinin lokacin da maharan suka mamaye ƙauyen, inda suka fara harbe-harbe kan mai uwa da wabi.

An buƙaci tsige shugaban APC na Kuros Riba Mai cutar HIV ya yi wa ’yar shekara 4 fyaɗe a Yobe

Wani mazaunin yankin da ya buƙaci a sakaya sunansa, ya ce maharan sun daɗe suna shigowa daga Jihar Kebbi suna kai hare-hare kan al’ummomin yankin.

“Sun saba zuwa daga Kebbi da Silame, suna kashe mutane ko su yi garkuwa da su. A wasu lokuta ma suna ɗora wa al’umma haraji, idan ba a biya cikin wa’adin da suka bayar ba, sai su kawo hari,” in ji shi.

Wata majiya ta bayyana cewa akwai wasu mutum biyu da suka jikkata sakamakon harbin bindiga da ke karɓar magani a wani asibiti da ke kusa da yankin.

Shugaban al’umma a yankin ya roƙi gwamnati ta kafa ofishin jami’an tsaro a yankin domin daƙile barazanar maharan, yana mai cewa yanzu babu ko ɗaya a yankin.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sanda ta Jihar Sakkwato, DSP Ahmad Rufa’i, ya ce bai samu rahoton lamarin ba tukuna, amma zai bincika.

Sai dai har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton, bai waiwayi Aminiya da wani ƙarin bayani ba.

Ƙauyen Alkalije na cikin gundumar Kilgori da ke iyaka da Ƙaramar Hukumar Silame da wasu ƙauyuka na Jihar Kebbi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nijeriya ta doke Gabon a wasan neman tikitin Kofin Duniya
  • Dalilin da ya kamata PDP ta jingine taron da za ta gudanar— Saraki
  • Dalilai 5 Da Suka Jefa Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa Ta Kano Pillars Cikin Matsaloli A Kakar Wasa Ta 2024/25
  • Jihar Kwara Ta Jaddada Kudirin Tallafa wa Wadanda Suka Tsira Daga Cin Zarafin Jinsi
  • Matasa 12 sun mutu a turmutsutsun neman aikin soja a Ghana
  • ’Yan sanda sun kama mutum 14 kan zargin ta’amali da miyagun ƙwayoyi a Jigawa
  • Babu wani gwamna da zai yi ƙorafin ƙarancin kuɗi a mulkin Tinubu — Sanwo Olu
  • ’Yan bindiga sun kashe mai juna biyu da wasu mutum 4 a Sakkwato
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3 A Nasarawa
  • Kotu Ta Sake Hana PDP Gudanar Da Babban Taronta Na Ƙasa