Dare da aka zubar da jini mafi muni a Gaza: Sama da Falasdinawa 80 ne suka yi shahada a sassa daban-daban na Zirin

Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da aiwatar da kisan kiyashi kan fararen hula a yankuna daban-daban na zirin Gaza, inda suka yi sanadiyyar shahadan sama da Falasdinawa 80, kuma mafi yawansu a wani kisan kiyashi da aka yi wa ‘yan gudun hijira a yankin Al-Mawasi na Khan Yunus da ke kudancin zirin Gaza, bayan da aka jefa bama-bamai da kona tantunansu a kusa da Asibitin kwararru na Kuwait, baya ga kisan kiyashi a duk fadin yankin.

Majiyoyin Falasdinawa sun ce an kona mutane 36, yawancinsu mata da kananan yara, bayan da sojojin mamayar Isra’ila suka yi ruwan bama-bamai a tantunansu, tare da cinna musu wuta. An kuma kai harin bama-bamai a gidaje hudu a yankin Abasan da biyu a Al-Fakhari.

Har ila yau sojojin mamayar sun kai hare-haren bama-bamai a wasu gidaje a tsakiyar zirin Gaza, inda suka kashe mutane 9 a Az-Zawayda da 3 a Deir al-Balah.

A arewacin Zirin Gaza, jiragen sama sojin mamayar sun kai hari kan gidajen fararen hula, inda suka kashe Falasdinawa 12 a gidan Nasser Jabalia al-Nazla, 8 a wani gida a Jabaliya al-Balad, da shahidai 7 a gidan al-Barawi a garin Beit Lahiya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP

Jami’an tsaro sun hana mambobin Kwamitin Amintattu na Jam’iyyar Adwa ta PDP gudanar da taron da suka tsara gudanarwa.

A safiyar Litinin din nan ne jami’ai da yawa ne suka kutsa cikin zauren da aka tsara gudanar da taron inda suka bukaci wadanda suka hallara da su watse.

Jami’an tsaro da aka jibge a hedikwatar babbar jam’iyyar adawar sun hana mambobin kwamitin amintattu gudanar da taronsu a hedikwatar jam’iyyar.

Har zuwa lokacin hada da wannan rahoto, wasu daga cikin ’yan kwamitin amintattun na PDP suna tattaunawa a kan halin da ake ciki.

Mun samu rahotannin cewa jami’an sun umurci mambohin su bar ofishin jam’iyar domin ganin ba a gudanar da wani taro a ofishin jam’iyar ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • Zambiya Ta Kaddamar Da Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Mafi Girma
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Sabani Tsakanin Bin Gafir, Smotresh Da Zamir Kan Makomar Fursinonin Yahudawa A Gaza
  • Gwamnan Bauchi zai ƙirƙiro sabbin masarautu
  • Dalibai 29 Suka Rasu A Turmutsitsin Tserewa Ga Fashewar Taransifoma A Jamhuriyar Afirka Ta Tsakiya
  • Jami’an tsaro sun tarwatsa taron kwamitin amintattun PDP
  • HKI Ta Kashe Falasdinawa 72 A Cikin Gaza A Yua Litinin
  • Iran: An Kama Wani Dan Leken Asirin “Mosad” A Tehran A Jiya Lahadi