Leadership News Hausa:
2025-05-30@17:46:05 GMT

Tabbaci Kan Bunkasuwar Tattalin Arziki Mai Dorewa A Sin

Published: 14th, March 2025 GMT

Tabbaci Kan Bunkasuwar Tattalin Arziki Mai Dorewa A Sin

Babban abin da ya bai wa Sin nasarar bunkasuwar tattalin arziki cikin sauri shi ne yadda gwamnati ta maida hankali wajen gina manyan ginshikai da tattalin arziki ke dogara da su domin samun ci gaba mai dorewa. Misali, irin layukan dogon da aka shimfida da suka sada ko wane lungu da sako a duk fadin kasar, da zamanantar da harkar sufurin jiragen sama da na ruwa, gami da bunkasuwar harkar yawon shakatawa ya janyo hankulan kasashen duniya tare da ba su kwarin gwiwa wajen rige-rigen zuwa Sin domin zuba jari.

Tattalin arziki na zamani yana tafiya tare da fasahar zamani, kuma a fannin kirkirarriyar fasaha, kasar Sin tana a sahun gaba. Domin idan ba’a manta ba, a kwanakin baya Sin ta samar da wata kirkirarriyar fasaha mai suna Deepseek, wadda ta bada al’ajabi ga duniya, musamman Turai da America. Har ta kai ga shugaba Trump ya yi kira da a taka birki ga Sin bisa ga yadda take ci gaba cikin sauri a duk fannoni.

Ta fannin inganta rayuwar ‘yan kasa kuwa, Sin ta cike gibin dake tsakanin birane da yankunan karkara. Ma’ana, duk abubuwan more jin dadin rayuwa da za ka samu birni, to akwai su a yankunan karkara. Wannan ya bada damar bunkasar tattalin arziki da zamantakewa masu dorewa a yankunan karkara.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC

Firaministan kasar Sin Li Qiang, ya yi kira ga aiwatar da matakai da za su zamo misali na bude kofa, da raya hadin gwiwa, da dunkule mabanbantan wayewar kai tsakanin Sin da ASEAN da GCC.

Li Qiang, ya bayyana hakan ne a Talatar nan, cikin jawabinsa ga bikin kaddamar da dandalin Sin da ASEAN da GCC, wanda aka bude a birnin Kuala Lumpur fadar mulkin kasar Malaysia.

Li, ya kuma yi kira ga sassan uku da su samar da wani salo na yin komai a bude tsakanin shiyyoyi, duba da cewa adadin al’ummunsu, da darajar tattalin arzikin da suke da shi ya kai rubu’in na duniya baki daya. Don haka dinkewar kasuwannin sassan 3, zai samar da babban fage na bunkasa da muhimmin tasirin da ake fata. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza
  • Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
  • Yuhudawan Sahayoniyya ‘Yan Kaka Gida Sun Kutsa Cikin Masallacin Al-Aqsah
  • Hadin Gwiwar Sin Da Yankin Turai Na Kara Kawo Haske Ga Tattalin Arzikin Duniya
  • Taron Kolin ASEAN Sin Da GCC Na Da Matukar Muhimmanci
  •  Arakci: Idan Birtaniya Ta Ci Gaba Da Batun Dakatar Da Tace Uranium A Iran, Za A Dakatar Da Tattaunawa Da Ita
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka
  • Sin Za Ta Kara Zurfafa Dunkule Rawar Yankunan Raya Tattalin Arziki Da Fasahohi A Fannin Janyo Jarin Waje
  • Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Nuna Misali Na Bude Kofa Da Raya Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da ASEAN Da GCC