Kwamatin duba Shirin samar da abincin buda baki na majalisar dokokin jihar Jigawa a shiyyar Dutse, ya yaba da kyakkyawan yanayin kosai da kunu da ake samarwa domin rabawa masu azumi a cibiyar bada abincin ta 2 a mazabar Kiyako ta karamar hukumar Birnin Kudu.

Shugaban Kwamatin kuma mataimakin Shugaban Majalisar, Alhaji Sani Isyaku Abubakar, ya bayyana haka a lokacin rangadin kwamatin.

Ya bayyana bubukatakarin kayan miya wajen dafa shinkafar da ake rabawa masu azumi.

Da ya ke mayar da jawabi, mai samar da abincin buda baki a cibiyar mazabar Kiyako da ke Babaldu, Salisu Sabo, ya ce suna samar da abincin buda baki da ya hada da shinkafa dafa-duka da kunu da kosai, ga masu azumi 300 a kowace rana.

Salisu Sabo ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa bullo da tsarin ciyar da masu azumi a fadin jihar.

Kwamatin ya Kai makamanciyar wannan ziyara garuruwan Wurno da Kiyako da kuma Birnin kudu.

Kazalika, ya ja hankalin mai aikin dafa abincin buda Baki a cibiyar Gantsa Yamma ya kara kayan miya da mai wajen dafa shinkafar da ake rabawa jama’a.

Ya yi wannan jan hankali ne lokacin da ya jagoranci ‘yan kwamatin domin duba Shirin Samar da abincin buda baki a karamar hukumar Buji, inda ya bukaci masu aikin raba abincin su rinka amfani da safar hannu domin tabbatar da tsafta.

Alhaji Sani Isayku Abubakar ya ce kwamatin yana rangadi ne domin tabbatar da ganin cewa masu aikin dafa abincin su na aiki da tsarin gwamnatin jihar Jigawan wajen dafa abincin da rabawa ga jama’a.

Sai dai kuma, ya yabawa mai aikin dafa abincin a Gantsa bakin Tasha bisa gudanar da aikinsa kamar yadda gwamnati ta bada umarni.

Da ya ke mayar da jawabi, mai aikin dafa abincin buda baki a Gantsa bakin Tasha Malam Sani Yusuf, ya ce ana ba su naira dubu 672 duk kwana uku domin dafa shinkafa kwano 10 da kunu na gero kwano 10 da kosai na wake kwano 10.

A nasa bangaren, Jami’in Shirin na karamar hukumar Buji, Malam Tasi’u Ibrahim Gantsa, ya ce an kafa cibiyoyi 20 a fadin karamar hukumar wadda ake bawa naira 672 cikin kwanaki uku domin Samar da shinkafa da kosai da kunu, bisa kudurin gwamnatin jiha na ciyar da jama’a a watan Azumi.

 

Usman Mohammed Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph

Majalisar Shura ta Jihar Kano ta fara zama da Malam Lawan Shu’aibu Abubakar (Triumph) kan zargin da wasu kungiyoyi biyar ke masa zargin batanci ga Manzon Allah SallalLahu alaihi Wasallama.

Wannan tattaunawa tana gudana ne a cikin sirri a Ofishin Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) kuma ya samu halarcin fitattun malaman Musulunci na Jihar Kano.

Mahalarta sun haɗa shugaban majalisar shurar  Malam Abba Koki da Wazirin Kano, Sa’ad Shehu Gidado, da sakatare, Shehu Wada Sagagi, da mambobin kwamitin da Majalisar Shurar ta kadfa domin zargin binciken zargin da ake wa Malam Triumph.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
  • Kungiyar (ASUU) Ta Sanar Da Shiga Yajin Aikin  Gargadi A Kasa Baki Daya .
  • Majalisar Shura ta fara ganawar sirri da Malam Triumph
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Kungiyar ‘Yan Dako Ta Kasa Ta Nada Sabon Sakatare A Jigawa
  • Afuwar Tinubu za ta buɗe hanyar ci gaba da aikata miyagun laifuka — Atiku
  • Za A Yi Wa Masu Lalurar Ido Aiki Kyauta A Jihar Jigawa
  • Macron Na Ci Gaba Da Shan Matsin Lamba Daga ‘Yan Adawa Da Tsofaffin Na Hannun Damansa
  • Al’ummar Karamar Hukumar Dutse Sun Bukaci Gwamnatin Jigawa Ta Yashe Madatsar Ruwa Ta Warwade
  • Wani Dan Majalisar Dokokin Kasar Iran Ya Ja Kunnen Amurka Kan Taba Jiragen Dakon Man Kasa