Kwamitin Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Na Ci Gaba Da Rangadi Cibiyoyin Ciyar Da Masu Azumi
Published: 14th, March 2025 GMT
Kwamatin duba Shirin samar da abincin buda baki na majalisar dokokin jihar Jigawa a shiyyar Dutse, ya yaba da kyakkyawan yanayin kosai da kunu da ake samarwa domin rabawa masu azumi a cibiyar bada abincin ta 2 a mazabar Kiyako ta karamar hukumar Birnin Kudu.
Shugaban Kwamatin kuma mataimakin Shugaban Majalisar, Alhaji Sani Isyaku Abubakar, ya bayyana haka a lokacin rangadin kwamatin.
Ya bayyana bubukatakarin kayan miya wajen dafa shinkafar da ake rabawa masu azumi.
Da ya ke mayar da jawabi, mai samar da abincin buda baki a cibiyar mazabar Kiyako da ke Babaldu, Salisu Sabo, ya ce suna samar da abincin buda baki da ya hada da shinkafa dafa-duka da kunu da kosai, ga masu azumi 300 a kowace rana.
Salisu Sabo ya yabawa Gwamna Umar Namadi bisa bullo da tsarin ciyar da masu azumi a fadin jihar.
Kwamatin ya Kai makamanciyar wannan ziyara garuruwan Wurno da Kiyako da kuma Birnin kudu.
Kazalika, ya ja hankalin mai aikin dafa abincin buda Baki a cibiyar Gantsa Yamma ya kara kayan miya da mai wajen dafa shinkafar da ake rabawa jama’a.
Ya yi wannan jan hankali ne lokacin da ya jagoranci ‘yan kwamatin domin duba Shirin Samar da abincin buda baki a karamar hukumar Buji, inda ya bukaci masu aikin raba abincin su rinka amfani da safar hannu domin tabbatar da tsafta.
Alhaji Sani Isayku Abubakar ya ce kwamatin yana rangadi ne domin tabbatar da ganin cewa masu aikin dafa abincin su na aiki da tsarin gwamnatin jihar Jigawan wajen dafa abincin da rabawa ga jama’a.
Sai dai kuma, ya yabawa mai aikin dafa abincin a Gantsa bakin Tasha bisa gudanar da aikinsa kamar yadda gwamnati ta bada umarni.
Da ya ke mayar da jawabi, mai aikin dafa abincin buda baki a Gantsa bakin Tasha Malam Sani Yusuf, ya ce ana ba su naira dubu 672 duk kwana uku domin dafa shinkafa kwano 10 da kunu na gero kwano 10 da kosai na wake kwano 10.
A nasa bangaren, Jami’in Shirin na karamar hukumar Buji, Malam Tasi’u Ibrahim Gantsa, ya ce an kafa cibiyoyi 20 a fadin karamar hukumar wadda ake bawa naira 672 cikin kwanaki uku domin Samar da shinkafa da kosai da kunu, bisa kudurin gwamnatin jiha na ciyar da jama’a a watan Azumi.
Usman Mohammed Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Ci gaba da killace Gaza da kuma kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, laifi ne da ba a taba yin irinsa ba a tarihin dan Adam
A wata tattaunawa ta wayar tarho da takwaransa na Masar Badar Abdel Ati a yammacin jiya Lahadin da ta gabata, Araqchi ya bayyana ci gaba da killace yankin Gaza da rashin abinci da magunguna, tare da kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba, a matsayin wani laifi da ba a taba ganin irinsa ba a tarihin dan Adam. Ya dauki Amurka da sauran masu goyon bayan ‘yan sahayoniyya a matsayin masu hannu a kisan kiyashi da laifukan yaki da ake aikatawa a Gaza.
Ministan harkokin wajen na Iran ya jaddada wajibcin tunkarar muggan manufofin yahudawan sahayoniyya na tilastawa al’ummar Gaza da yammacin kogin Jordan yin hijira daga muhallinsu, yana mai bayyana halin ko in kula da kasashen duniya suke nun awa kan wadannan laifuka a matsayin abin mamaki da damuwa.
Araghchi ya kuma yi wa takwaransa na Masar bayani kan ci gaban tattaunawar Iran da Amurka kan Shirin makamashin nukiliya na zaman lafiya da ake takaddama a kai tsawon shekaru.