Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?
Published: 18th, May 2025 GMT
Babbar Jam’iyyar hamayya ta PDP ta ce, ta soma ɗaukar matakan ɗinke ɓarakar da ta dabaibaye ta a ’yan shekarun nan.
Matakin baya-bayan nan shi ne na taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar ta gudanar.
Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon FafaromaShin ko hakan zai kawo ƙarshen matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan faɗuwa zaɓen 2023?
Daga cikin matsalolin da suka kunno kai a cikin babbar Jam’iyyar adawa ta PDP tun bayan faduwarta zaɓe a 2023 shi ne yin baram-baram a kan yadda za ta dinke barakar da aka samu a lokacin zaben fidda-gwani da rikicin shugabanci a matakai daban-daban da kuma kasa tsayawa da kafarta domin samar da adawa mai nagarta a siyasar kasar nan.
Sau tari dai an sha jin masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar na cewa, suna ƙoƙarin ɗinke ɓarakar tasu da kuma dawowa da ƙarfi, har ma a wasu lokutan sukan sha alwashin ƙwace mulki daga hannun Jam’iyyar APC.
A tsakanin ranar Lahadi da daddare zuwa wayewar garin Litinin da suka gabata ma an ga yadda masu ruwa da tsaki a Jam’iyyar ta PDP ɗin suka yunƙura domin samar da mafita ga ɗimbin matsalolin nasu, inda har suka kafa kwamitin da zai jagoranci cim ma nasarar hakan.
Tuni dai masana harkokin siyasa, irin su Dakta Yakubu Haruna Ja’e na Jami’ar Jihar Kaduna suka fara sharhi a kan wannan batu.
Ya ce, gaskiya abu ne da ya kamata a ce sun yi shi tun a baya duk da kuma cewa akwai barazana mai ƙarfi da ke fuskantar su, kasancewa shi Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ɗan Jam’iyyar APC ne ɗan siyasa kuma yana zagaye da ’yan siyasa da suke ƙoƙarin ganin sun janyo duk wani mutum daga cikin duk wata jam’iyya da take fama da rikicin cikin gida da domin ya bar ta, ya dawo cikin ita Jam’iyya mai mulki ta APC.
Dangane da hasashen da ake ta yi cewa, ’yan adawar ciki har da PDP suna neman kulla hadaka domin fuskantar zaben 2027 kuwa, Yakubu Ja’e na ganin cewa har yanzu ba a makara ba.
Ya ce, ‘‘shugaban da yake kai gaskiya yana da ƙarfi duk da ana ganin kamar ba a son sa, amma yana da abin da zai sa a so shi saboda yana da kuɗi mutane kuma ba a raba su da kuɗi idan siyasa ta taso.
To amma idan da waɗannan jam’iyyu za su iya haɗa kai ƙwarai da gaske, za su iya kaiwa ga nasara tun da aƙalla idan ka lura masoya APC sun yi rauni a wasu manyan jihohi kusan biyar, domin ka ga sam ba ta ci zaɓe a Jihar Legas ba, kuma sun samu rauni, kuma har yanzu suna da wannan raunin, ga Jihar Ribas abin da suka yi na cire zaɓaɓɓen gwamna suna sa nasu wannan zai iya sa su rasa jihar, ga Kano shi ma haka ne ga ma Kaduna haka ne.
“To idan ka dubi wadannan manyan jihohi lallai da Jam’iyyar PDP za ta haɗa kai da wasu jam’iyyu zai iya ba ta dama ta ci zabe in an cire kwadayi’’.
Me ya janyo jinkiri wajen ɗinke ɓarakar PDP ɗin?
Sanata Umar Tsauri, mamba ne a kwamitin amintattu na jam’iyyar cewa ya yi, Jam’iyyar PDP ta yi amanna cewa ko yanzu aka shiga zabe tana da hajar tallata wa al’ummar kasar nan.
“Ba za ka iya gane mutum fari ba ne sai akwai baƙi a tare da shi; ba za ka iya gane mutum gajere ba ne sai akwai dogo a tare da shi.
“Idan mutane suka kwatanta yadda mulkin Jam’iyyar APC na shekara biyu ya kasance da kuma mulkin PDP na shekara 16 sai su yanke wa kansu hukunci,’’ in ji shi.
Masu sharhi dai na ganin cewa, duk wadannan dabaru da salon tade kafafun juna da ke gudana a tsakanin jam’iyyun siyasar ba su wuce fafutukar neman mulki a 2027 ba, wanda kuma lokaci ne kawai zai iya tabbatar da bangaren da ya fi iya allonsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɓaraka zaɓen 2023 Zaɓen 2027 a Jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu ɗauki mataki kan mambobinmu da ke shirin shiga haɗakar ADC — PDP
Babbar jam’iyyar hamayya a Nijeriya, PDP ta ce za ta ɗauki tsattsauran mataki kan mambobinta da ke ƙoƙarin shiga sabuwar haɗaka da jam’iyyar ADC.
Yayin da yake jawabi ga manema labarai bayan taron kwamitin amintattun jam’iyyar, shugaban jam’iyyar na ƙasa Ambasada Iliya Damagum ya ce jam’iyyar tana gargaɗi ’yan’yanta da ke shirin shiga sabuwar haɗakar ADC.
Damagum ya ce ƙoƙarin da haɗakar ke shirin yi ba zai yi tasiri ba, yana mai cewa da dama daga cikin mambobin haɗakar za su koma jam’iyyunsu.
“Yana da kyau su sani cewa babu inda ya kamata a haɗu domin tunkarar gwamnatin APC da ya wuce jam’iyyar PDP, amma in suna ganin ba haka ba, to su je su gwada su gani, amma dai na san dole za su dawo”, in ji shi.
Shugaban riƙon ya kuma gargaɗi ’yan PDP da ya ce suna ƙoƙarin “sayar da jam’iyyar”.
Kawo yanzu dai akwai jiga-jigan PDP cikin sabuwar haɗakar ta ADC, ciki har da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar a zaɓen da ya gabata, Atiku Abubakar.
A farkon makon nan ne dai jam’iyyar PDP ta gudanar da taronta na Kwamitin Zartaswa da a ciki ta ce ta ɗinke ɓarakar da ta ɗauki tsawon lokacin tana fama da ita a cikin jam’iyyar.
Mun shirya fito-na-fito da APC — MalamiShi ma dai tsohon Ministan Shari’a, Abubakar Malami ya ce a shirye haɗakar ADC take wajen yaƙi da gwamnatin APC domin kawo “gyara kan yadda ake tafiyar da gwamnati.”
Malami —wanda ya kasance minista a zamanin gwamnatin tsohon shugaban Nijeriya, Mumammadu Buhari — ya ce ukuɓar da gwamnati Tinubu ta sanya talakawan Nijerya a ciki ba za ta misaltu ba.
A hirarsa da BBC, Abubakar Malami ya ce sun fito fili ne domin su yaƙi jam’iyyar APC mai mulki, musamman yadda ta bar abubuwa da dama sun tabarbare a ƙasar, ciki har da tsaro da tattalin arziki da kuma sauran dangogin wahalhalu da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta jefa talakawa.
“A duk lokacin da wata tarayya ta zo da wasu tsare-tsare na ƙuntata wa al’umma, da sanya su cikin halin wahala to wajibi a taru wuri guda su dauki mataki domin kawo sauyi ta hanyar maido da kaykkyawan tsari, da zai ɗaɗa wa mutane”, in ji shi.
“Mun yanke hukuncin ɗaukar mataki domin yaƙi da rashin tsaro da ynuwa domin maido da Nijeriya kan turba mai kyau da tsari”, in ji Malami.