Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?
Published: 18th, May 2025 GMT
Babbar Jam’iyyar hamayya ta PDP ta ce, ta soma ɗaukar matakan ɗinke ɓarakar da ta dabaibaye ta a ’yan shekarun nan.
Matakin baya-bayan nan shi ne na taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar ta gudanar.
Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon FafaromaShin ko hakan zai kawo ƙarshen matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan faɗuwa zaɓen 2023?
Daga cikin matsalolin da suka kunno kai a cikin babbar Jam’iyyar adawa ta PDP tun bayan faduwarta zaɓe a 2023 shi ne yin baram-baram a kan yadda za ta dinke barakar da aka samu a lokacin zaben fidda-gwani da rikicin shugabanci a matakai daban-daban da kuma kasa tsayawa da kafarta domin samar da adawa mai nagarta a siyasar kasar nan.
Sau tari dai an sha jin masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar na cewa, suna ƙoƙarin ɗinke ɓarakar tasu da kuma dawowa da ƙarfi, har ma a wasu lokutan sukan sha alwashin ƙwace mulki daga hannun Jam’iyyar APC.
A tsakanin ranar Lahadi da daddare zuwa wayewar garin Litinin da suka gabata ma an ga yadda masu ruwa da tsaki a Jam’iyyar ta PDP ɗin suka yunƙura domin samar da mafita ga ɗimbin matsalolin nasu, inda har suka kafa kwamitin da zai jagoranci cim ma nasarar hakan.
Tuni dai masana harkokin siyasa, irin su Dakta Yakubu Haruna Ja’e na Jami’ar Jihar Kaduna suka fara sharhi a kan wannan batu.
Ya ce, gaskiya abu ne da ya kamata a ce sun yi shi tun a baya duk da kuma cewa akwai barazana mai ƙarfi da ke fuskantar su, kasancewa shi Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ɗan Jam’iyyar APC ne ɗan siyasa kuma yana zagaye da ’yan siyasa da suke ƙoƙarin ganin sun janyo duk wani mutum daga cikin duk wata jam’iyya da take fama da rikicin cikin gida da domin ya bar ta, ya dawo cikin ita Jam’iyya mai mulki ta APC.
Dangane da hasashen da ake ta yi cewa, ’yan adawar ciki har da PDP suna neman kulla hadaka domin fuskantar zaben 2027 kuwa, Yakubu Ja’e na ganin cewa har yanzu ba a makara ba.
Ya ce, ‘‘shugaban da yake kai gaskiya yana da ƙarfi duk da ana ganin kamar ba a son sa, amma yana da abin da zai sa a so shi saboda yana da kuɗi mutane kuma ba a raba su da kuɗi idan siyasa ta taso.
To amma idan da waɗannan jam’iyyu za su iya haɗa kai ƙwarai da gaske, za su iya kaiwa ga nasara tun da aƙalla idan ka lura masoya APC sun yi rauni a wasu manyan jihohi kusan biyar, domin ka ga sam ba ta ci zaɓe a Jihar Legas ba, kuma sun samu rauni, kuma har yanzu suna da wannan raunin, ga Jihar Ribas abin da suka yi na cire zaɓaɓɓen gwamna suna sa nasu wannan zai iya sa su rasa jihar, ga Kano shi ma haka ne ga ma Kaduna haka ne.
“To idan ka dubi wadannan manyan jihohi lallai da Jam’iyyar PDP za ta haɗa kai da wasu jam’iyyu zai iya ba ta dama ta ci zabe in an cire kwadayi’’.
Me ya janyo jinkiri wajen ɗinke ɓarakar PDP ɗin?
Sanata Umar Tsauri, mamba ne a kwamitin amintattu na jam’iyyar cewa ya yi, Jam’iyyar PDP ta yi amanna cewa ko yanzu aka shiga zabe tana da hajar tallata wa al’ummar kasar nan.
“Ba za ka iya gane mutum fari ba ne sai akwai baƙi a tare da shi; ba za ka iya gane mutum gajere ba ne sai akwai dogo a tare da shi.
“Idan mutane suka kwatanta yadda mulkin Jam’iyyar APC na shekara biyu ya kasance da kuma mulkin PDP na shekara 16 sai su yanke wa kansu hukunci,’’ in ji shi.
Masu sharhi dai na ganin cewa, duk wadannan dabaru da salon tade kafafun juna da ke gudana a tsakanin jam’iyyun siyasar ba su wuce fafutukar neman mulki a 2027 ba, wanda kuma lokaci ne kawai zai iya tabbatar da bangaren da ya fi iya allonsa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɓaraka zaɓen 2023 Zaɓen 2027 a Jam iyyar
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Ya kara da cewa, ana ci gaba da kokari don ganin an iske masu yin kiwon shanu a kasar nan, domin fadakar da su kan muhimmancin rungumar wannan tsari na zamani.
Sai dai, ya yi nuni da cewa; wasu al’adu na haifar da tarnaki a tsakanin wasu masu kiwon a kasar na rungumar wannan tsarin.
“Na ga wasu gidajen gona da ake yin irin wannan dabara ta zamani, sannan kuma ana bayar da kulawar da ta kamata; wanda hakan ya sanya ake iya samar da litar madarar shanu daga tsakanin lita 15 zuwa 30,” in ji Jatau.
“Akwai wasu Fulani Makiyaya ‘yan kalilan da suka rungumi wannan tsari, misali a Jihar Bauchi; inda wani makiyayi ya rungumi wannan tsari tare kuma da amfanarsa yadda ya kamata,” a cewarsa.
“A lokacin da muka gudanar da ayyukanmu, wasu daga cikin Fulani Makiyaya, sun zo sun saurari wannan batu na dabara ta zamani tare da shanunsu, mun kuma aiwatar da tsarin a kan shanun nasu, inda daga baya suka ga yadda madarar shanunsu ta kara habaka,” in ji shi.
Jatau ya kara da cewa, suna kan ci gaba da bai wa Fulani Makiyaya kwarin guiwa, kan rungumar wannnan tsari, sai dai, wasu na fuskantar kalubale na kula da shanunsu da aka dora su a kan tsarin.
“A wasu kasashen na Afirka za ka cewa, Makiyayin da suka rungumi wannan tsari, na da shanu uku ne kacal da daukacin iyakansa suka dogara a kansu, wanda hakan ke ba su dama a kullam na samar da litar madara daga tsanakin 15 zuwa 20, “ a cewarsa.
Ya kara da cewa, hakan ya sanya a kullum suke samar wa da kansu dimbin riba, wanda kuma hakan ya sa ba su dogaro da aikin gwamnati ba kwata-kwata.
Ya yi nuni da cewa, idan har a raba daya za ka sayar da litar madara daya kan Naira 1,000, a wata za ka iya samun kudin shiga da suka kai Naira miliyan 1.8 da shanu uku kacal.
Ya ci gaba da cewa, da wannan ribar kadai za ka iya ci gaba da ciyar da shanun da lula da lafiyarsu da biyan ma’aikatan da ke kula da su da kuma daukar sauran dawainiyar kula da iyalanka.
Ya bayyana cewa, duba da cewa; ana fuskantar matsalar wajen da dabbobi za su yi kiwo a kasar nan, amma idan Fulani Makiyaya suka rungumi wannan tsari, hakan zai rage yawan samu rikice-rikice a tsakanin manoma da Fulani Makiyya a kasar.
Kazalika, ya sanar da cewa; idan masu kiwon suka dauki wannan tsari za a samu cewa, alfanun da za su samu ya dara irin na kiwon gargajiya da ake yi a cikin kasar.
Jatau ya bayyana cewa, wannan tsarin abu ne da ke da tsawon tarihi a kasar nan, domin an faro shi ne tun a shekarar 1949; tun bayan da aka dauki nau’in na jinsin daga wata gona da ke garin Shika a birnin Zaria, aka kuma kai shi zuwa cibiyar gudanar da bincike kan lafiyar dabbobi ta Bom.
Sai dai, ya bayyana cewa; rashin ci gaba da bibiyar wannan tsare-tsaren daga bangaren gwamnati, hakan ya haifar da koma baya ga wannan tsair.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA