Aminiya:
2025-05-18@12:26:04 GMT

Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?

Published: 18th, May 2025 GMT

Babbar Jam’iyyar hamayya ta PDP ta ce, ta soma ɗaukar matakan ɗinke ɓarakar da ta dabaibaye ta a ’yan shekarun nan.

Matakin baya-bayan nan shi ne na taron masu ruwa da tsaki da jam’iyyar ta gudanar.

Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma

Shin ko hakan zai kawo ƙarshen matsalolin da jam’iyyar ke fuskanta tun bayan faɗuwa zaɓen 2023?

Daga cikin matsalolin da suka kunno kai a cikin babbar Jam’iyyar adawa ta PDP tun bayan faduwarta zaɓe a 2023 shi ne yin baram-baram a kan yadda za ta dinke barakar da aka samu a lokacin zaben fidda-gwani da rikicin shugabanci a matakai daban-daban da kuma kasa tsayawa da kafarta domin samar da adawa mai nagarta a siyasar kasar nan.

Sau tari dai an sha jin masu ruwa da tsaki a cikin jam’iyyar na cewa, suna ƙoƙarin ɗinke ɓarakar tasu da kuma dawowa da ƙarfi, har ma a wasu lokutan sukan sha alwashin ƙwace mulki daga hannun Jam’iyyar APC.

A tsakanin ranar Lahadi da daddare zuwa wayewar garin Litinin da suka gabata ma an ga yadda masu ruwa da tsaki a Jam’iyyar ta PDP ɗin suka yunƙura domin samar da mafita ga ɗimbin matsalolin nasu, inda har suka kafa kwamitin da zai jagoranci cim ma nasarar hakan.

Tuni dai masana harkokin siyasa, irin su Dakta Yakubu Haruna Ja’e na Jami’ar Jihar Kaduna suka fara sharhi a kan wannan batu.

Ya ce, gaskiya abu ne da ya kamata a ce sun yi shi tun a baya duk da kuma cewa akwai barazana mai ƙarfi da ke fuskantar su, kasancewa shi Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ɗan Jam’iyyar APC ne ɗan siyasa kuma yana zagaye da ’yan siyasa da suke ƙoƙarin ganin sun janyo duk wani mutum daga cikin duk wata jam’iyya da take fama da rikicin cikin gida da domin ya bar ta, ya dawo cikin ita Jam’iyya mai mulki ta APC.

Dangane da hasashen da ake ta yi cewa, ’yan adawar ciki har da PDP suna neman kulla hadaka domin fuskantar zaben 2027 kuwa, Yakubu Ja’e na ganin cewa har yanzu ba a makara ba.

Ya ce, ‘‘shugaban da yake kai gaskiya yana da ƙarfi duk da ana ganin kamar ba a son sa, amma yana da abin da zai sa a so shi saboda yana da kuɗi mutane kuma ba a raba su da kuɗi idan siyasa ta taso.

To amma idan da waɗannan jam’iyyu za su iya haɗa kai ƙwarai da gaske, za su iya kaiwa ga nasara tun da aƙalla idan ka lura masoya APC sun yi rauni a wasu manyan jihohi kusan biyar, domin ka ga sam ba ta ci zaɓe a Jihar Legas ba, kuma sun samu rauni, kuma har yanzu suna da wannan raunin, ga Jihar Ribas abin da suka yi na cire zaɓaɓɓen gwamna suna sa nasu wannan zai iya sa su rasa jihar, ga Kano shi ma haka ne ga ma Kaduna haka ne.

“To idan ka dubi wadannan manyan jihohi lallai da Jam’iyyar PDP za ta haɗa kai da wasu jam’iyyu zai iya ba ta dama ta ci zabe in an cire kwadayi’’.

Me ya janyo jinkiri wajen ɗinke ɓarakar PDP ɗin?

Sanata Umar Tsauri, mamba ne a kwamitin amintattu na jam’iyyar cewa ya yi, Jam’iyyar PDP ta yi amanna cewa ko yanzu aka shiga zabe tana da hajar tallata wa al’ummar kasar nan.

“Ba za ka iya gane mutum fari ba ne sai akwai baƙi a tare da shi; ba za ka iya gane mutum gajere ba ne sai akwai dogo a tare da shi.

“Idan mutane suka kwatanta yadda mulkin Jam’iyyar APC na shekara biyu ya kasance da kuma mulkin PDP na shekara 16 sai su yanke wa kansu hukunci,’’ in ji shi.

Masu sharhi dai na ganin cewa, duk wadannan dabaru da salon tade kafafun juna da ke gudana a tsakanin jam’iyyun siyasar ba su wuce fafutukar neman mulki a 2027 ba, wanda kuma lokaci ne kawai zai iya tabbatar da bangaren da ya fi iya allonsa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɓaraka zaɓen 2023 Zaɓen 2027 a Jam iyyar

এছাড়াও পড়ুন:

Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC

Shugaban Jam’iyyar APC na ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje ya ziyarci zauren Majalisar Wakilai a ranar Alhamis domin ganewa idanunsa ficewar wasu mambobi biyu na Jam’iyyar adawa ta NNPP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC.

’Yan majalisar biyu, sun haɗa da: Dan Majalisar Wakilai, Abdullahi Sani Rogo mai wakiltar mazaɓar Rogo/Karaye da kuma Ɗan Majalisar Wakilai Kabiru Alhassan Rurum mai wakiltar mazaɓar tarayya ta Rano/Bunkure/Kibiya, sun sauya sheƙa a ranar Alhamis.

Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a Filato Dalilin da ya sa gwamna Bala ya yi ƙoƙarin mari na – In ji Minista

Hakazalika mamba mai wakiltar mazaɓar Ijesha Oriade/Obokun na Jihar Osun, Wole Oke, ya kuma bayyana ficewarsa daga jam’iyyar adawa ta PDP zuwa APC.

Shugaban Majalisar Wakilai Tajudden Abbas  wanda ya sanar da sauya sheƙar, ya bayyana cewa mambobin sun bayyana dalilansu na ficewa daga jam’iyyarsu zuwa APC.

Sai dai Babban mai tsawatarwa na Marasa Rinjaye, Isa Ali JC, ya nuna rashin amincewarsa da cewa sauya sheƙar ya sabawa kundin tsarin mulkin ƙasar.

Ganduje wanda ya samu rakiyar wasu jami’an jam’iyyar, ya fice bayan sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zubar Da Jini Mafi Muni A Cikin Daren Jiya A Zirin Gaza, Inda Falasdinawa 80 Suka Yi Shahada
  • Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno
  • Chadi: An Kama Tsohon Fira Minista Kuma Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasa
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba
  • Kwankwaso ya fice daga NNPP tun a 2023 — Shugaban jam’iyya
  • A Tsammaci Garambawul Ga Dokar Zabe Kafin Zaben 2027 — Shugaban INEC
  • Dalilin Tsame Daya Cikin Uku Na Ma’aikatan Ƙasar Nan A Tsarin Sauye-sauyen Biyan Haraji – Czar
  • NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
  • Ganduje ya halarci Majalisar Wakilai don sheda ’Yan Majalisa 2 zuwa APC