’Yan bindiga sun sace mutum 10 da raunata 2 a Kaduna
Published: 13th, March 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne sun yi garkuwa da wasu ’yan ƙauye su goma daga wasu unguwanni uku da ke ƙarƙashin ƙaramar hukumar Kajuru ta Jihar Kaduna.
Lamarin ya faru ne a daren ranar Larabar, da misalin ƙarfe 2 na tsakar dare inda wasu gungun ’yan bindiga suka kai farmaki a unguwar Unguwan Yashi-Maraban Kajuru tare da yin garkuwa da mutane shida.
Waɗanda aka sace su ne: God-Dream Ladan, Lady God-Dream, Philip Mudakas, Mercy Philip, Bitrus Philip, da Gmen Philip.
Hakazalika, a ƙauyen Makyali, wasu mutane biyu sun samu raunuka na harbin bindiga, kuma a halin yanzu ana jinyarsu a asibitin Maraban Kajuru bayan ’yan bindiga sun kai wa unguwar hari.
An kuma yi garkuwa da wasu mata biyu Rahina Yahaya da Zulai Yahaya a ƙauyen. Waɗanda suka jikkata dai sun haɗa da: Ubale Yahaya da Abdullahi.
An samu rahoton cewa gungun ’yan bindigan sun koma Ungwan Mudi Doka da misalin ƙarfe 4 na asubahi inda suka yi garkuwa da wasu mutane biyu – Amos Michael da Samita Amos.
Muƙaddashin Hakimin Kufana, Stephen Maikori ya tabbatarwa Aminiya faruwar lamarin a ranar Alhamis, inda ya ce a baya-bayan nan an samu raguwar kai hare-haren, amma kuma a cikin makon nan ne suka sake kunno kai.
“Ya zuwa yanzu, an tafi da mutane goma, yayin da biyu suka samu raunuka, yanzu suna karɓar magani. Muna roƙon a ƙara ɗaukar matakan tsaro cikin gaggawa da ɗaukar matakin ceton rayuka da dukiyoyi a cikin wannan yankin,” in ji shi.
Ya kuma ƙara da cewa an kai rahoton faruwar lamarin ga hukumomin tsaro a kan lamarin. A halin da ake ciki dai har yanzu gwamnatin jihar da rundunar ’yan sanda ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, DSP Mansir Hassan, an kasa samunsa ta wayar tarho har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Bindiga yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu
Hukumomin ’yan sandan Najeriya tare da haɗin gwiwar wasu hukumomin tsaro sun samu gagarumar nasara a ƙoƙarin da suke na daƙile munanan laifuka a ƙasar.
Na baya-bayan nan dai shi ne ceto mutanen da aka sace, da kashe wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne da kuma ƙwato manyan bindigogi da alburusai a jihohin Delta da Katsina.
Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a AustraliaA wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan, Olumuyiwa Adejobi ya fitar, ya ce a jihar Katsina an samu gagarumar nasara a ranar 8 ga watan Yunin 2025, inda haɗin gwiwar JTF da suka haɗa da jami’an ’yan sanda da sauran jami’an tsaro suka daƙile wani yunƙurin yin garkuwa da mutane a hanyar ƙauyen Danmusa zuwa Mara Dangeza a ƙaramar hukumar Danmusa.
Adejobi ya ce hakan na iya yiwuwa ne ta hanyar shigar da wasu gungun ’yan bindiga da suka yi yunƙurin guduwa da waɗanda aka yi garkuwa da su a wani artabu da ya kai ga ceto mutum 11.
Nasarar da aka samu yankin Kudu maso KuduA halin da ake ciki kuma, a yankin Kudu maso Kudu, Jihar Delta, hukumar ’yan sanda ta kama wani Abubakar Hassan, wanda babban wanda ake zargi da aikata laifin satar mutane ne a tsakanin jihohin Delta da Ribas da Imo, da Enugu.
Jami’an da ke da alaƙa da samun nasarar sun yi hakan ne yayin da suke aiki da sahihan bayanai.
A yayin da ake yi masa tambayoyi, Hassan ya bayyana cewa shi ne ya jagoranci gudanar da hari a yankin Ughelli-Ozoro na jihar mai arzikin man fetur.
Ya kuma jagoranci jami’an ’yan sanda zuwa maɓoyarsa a wani daji da ke Ozoro. A can jami’an sun ƙwato bindigogi ƙirar AK-47 guda biyu da tarin alburusai huɗu da harsashi guda talatin da biyu.