Tattalin Arzikin Kasar Sin Ya Bunkasa Duk Da Matsaloli Da Dama
Published: 20th, May 2025 GMT
Bayan da mahukuntan kasar Sin suka kaddamar da yadda harkokin tattalin arzikin kasar suka gudana a watan Afrilun bana a ranar 19 ga wata, mataimakin shugaban zartaswa na kamfanin Novonesis na kasar Denmark, Morten Enggaard Rasmussen ya tattauna da wakilin CMG, inda a cewarsa, alkaluma sun nuna karfin tattalin arzikin kasar Sin.
A watanni 4 na farkon bana, saurin karuwar muhimman alkaluma masu alaka da samar da kaya a kasar Sin ya fi na shekarar bara baki daya. A watan Afrilu, wasu 36 daga cikin manyan sana’o’i 41 sun samu ci gaba bisa na makamancin lokacin a bara, adadin da ya wuce 80%. Alkaluma sun kuma nuna cewa, duk da matsalolin da take fuskanta, kasar Sin ta raya tattalin arzikinta ba tare da tangarda ba cikin watanni 4 na farkon bana, kuma ci gabanta bai tsaya ba, lamarin da ya nuna juriya mai karfi na tattalin arzikin kasar da kuma yadda take tinkarar kalubale.
Ban da haka kuma, cinikayyar waje ta kasar Sin ta samu karuwa ba tare da matsala ba, yayin da Amurka ta dora wa kayan kasar Sin karin haraji, lamarin da ya nuna karfin kasar Sin na yin takara a duniya. A watanni 4 na farkon bana, saurin karuwar jimillar kayayyakin shige da fice a kasar Sin ya fi na watanni 3 na karshen shekarar 2024 sauri har da 1.1%, jimillar kayayyakin da aka fitar ta karu da 7.5%. Har ila yau, yawan motoci da kasar Sin ta kera da kuma sayar da su duk sun wuce miliyan 10 a karon farko.
Wannan shi ne dalilin da ya sa ake cewa, yin tafiya tare da kasar Sin, yin tafiya ne tare da damammaki. Kamar yadda shugaba Xi Jinping na kasar Sin ya fada cikin amsar wasikar da ya aike ga jagoran majalisar bunkasa cinikayya ta Denmark dake kasar Sin, yadda ake nuna wa kasar Sin karfin zuciya, ya yi kama da yadda ake nuna karfin zuciya kan kyakkyawar makoma. Kana zuba wa kasar Sin jari, zuba jari ne a kan makoma. (Tasallah Yuan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: tattalin arzikin kasar Sin kasar Sin ya a kasar Sin
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana
Hukumar Kula da Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta sanar da kammala dawo da dukkan alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana gida Najeriya daga kasar Saudiyya.
A cikin wata sanarwar da Daraktar Yaɗa Labarai ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta fitar ranar Laraba, ta ce jirgin karshe dauke da alhazai 88 ya bar birnin Jiddah da misalin karfe 10:30 na safe dauke da alhazan jihar Kaduna da Katsina.
Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a DeltaA cewar hukumar, hakan ya kawo karshen jigilar da aka shafe kwana 20 ana yi tun ranar 13 ga watan Yuni.
A sakonsa na bankwana ga alhazan, shugaban NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya bayyana godiyarsa ga Allah kan kammala aikin cikin nasara.
Ya kuma bukaci alhazan da su ci gaba da yi wa Najeriya addu’ar Allah ya kawo mata karshen tarin matsalolin da suke addabar ta.
Farfesa Abdullahi ya kuma tunatar da su cewa Aikin Hajji ibada ce da take nuna zaman lafiya da kwanciyar hankali, sannan ya buƙace su da su ci gaba da zumuncin da suka ƙulla a tsakaninsu lokacin ibadar.