Leadership News Hausa:
2025-05-19@22:36:40 GMT

Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600

Published: 19th, May 2025 GMT

Sin Ta Cimma Nasarar Gwajin Jirgin Sama Samfurin AG600

Kamfanin kirar jiragen sama na kasar Sin wato AVIC ya ce ya cimma nasarar samar da jirgin sama dake iya tashi a kasa da ruwa irinsa na farko samfuri AG600 da aka yiwa lakabi da “Kun Long”. An kuma cimma nasarar gwajinsa a jiya Lahadi a birnin Zhuhai na lardin Guangdong.

Hakan ya nuna cewa, ingancin jirgin ya dace da ma’aunin da aka tanada, kuma ya alamta cewa jirgin samfuri AG600 ya samu iznin kira wato PC.

Rahotanni na cewa a ranar 20 ga watan Afrilun bana, jirgin samfurin AG600 ya samu takardar shaidar inganci ta samfurinsa, matakin da ya nuna cewa, nazarin da aka yi a wannan bangare ya cimma cikakkiyar nasara, kuma jirgin ya samu izinin shiga kasuwa. Kazalika, kamfanin AVIC zai gaggauta tabbatar da cewa “Kun Long”, ya taka rawa a fannin ba da agajin gaggawa, da tinkarar da kuma kandagarkin bala’u daga indallahi. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno

Aƙalla manoma 50 ne suka rasu, sakamakon wani mummunan hari da ‘yan ta’addan ISWAP suka kai garin Malam Karanti da ke Ƙaramar Hukumar Kukawa, a jihar Borno.

Majiyoyi sun ce mayaƙan sun afka wa manoma yayin da suke noma da kamun kifi, duk da cewar suna biyan haraji kafin yin noma.

Tinubu ya isa Rome don rantsar da sabon Fafaroma Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani

“Sun mallaki takardun izini daga kwamandan ISWAP da ke kula da yankin Malam Karanti har zuwa Dawashi. Sun jima suna samun kariya daga Amir Akilu, wanda shi ne kwamandan yankin,” in ji wani mazaunin yankin.

Sai dai harin ya faru ne a lokacin da kwamandan bai kasance a yankin ba, inda wasu daga cikin mayaƙan suka zargi manoman da leƙen asiri, inda suka ce suna taimaka wa abokan gabansu.

Wannan ne dalilin da ya sa suka kai harin.

Wani wanda ya tsallake rijiya da baya a harin ya ce: “Mun fara girbin wake ne lokacin da suka zo. Sun kewaye mu, suka ce duk wanda ya yi yunƙurin tserewa za su harbe shi.

“Wasu daga cikinmu sun yanke shawarar guduwa duk da hakan. Sun kashe sama da mutum 50, da yawa daga cikinsu an yanka su.

“Sannan sun kama wasu daga cikinmu. Yau ma sun je Dawashi sun kashe mutane, amma ba a san adadin waɗanda suka kashe ba tukuna.”

Gwamnati da hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa dangane da wannan mummunan hari ba.

Wannan hari ya zo cikin watanni biyar kacal bayan wani makamancin sa da aka kai ƙauyen Dumba, inda manoma aƙalla 40 suka rasa rayukansu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An cimma matsaya kan dakatar da haska fina-finai 22 a Kano
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Bisa Daidaito A Afirilu
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su
  • Mutane 7 Sun Mutu 11Sun Jikkata A Hadarin Mota A Niger.
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Fatan Tattaunawar Kasarsa Da Amurka Ta Cimma Yarjejeniya Ta Gaskiya
  • Sojan Lebanon Daya Ya Jikkata Sanadiyyar Harin Sojan HKI Da Jirgin Sama Maras Matuki
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Saman Ben Gurion Na Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Iran ta ce babu wata rubutaciyar shawara da ta samu daga Amurka