A ɓangare guda kuma, kotu ta samu Natasha Akpoti-Uduaghan da laifin saɓawa umarnin kotu ta hanyar rubutun zaulaya da ta yi a shafinta na Facebook a ranar 7 ga watan Aprilu, inda take bayar da haƙuri amma ta hanyar zaulaya ga shugaban majalisar dattawa, Godswill Alpabio.

Kotun ta ce rubutun cin fuska ne ga umarninta, sannan ta umarci Natsha da ta rubuta saƙon bayar da haƙuri a shafukan jarida guda biyu da shafinta na Facebook.

Har ila yau, kotun ta ci tarar Natsha naira miliyan biyar bisa rubutun da ta wallafa a shafin na ta na Facebook.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba

Majalisar Dokokin Jihar Filato ta zaɓi Nanloong Daniel a matsayin sabon Kakakin Majalisar, bayan da Gabriel Dewan ya yi murabus.

Zaɓen sabon kakakin ya gudana ne a wani zaman gaggawa da majalisar ta gudanar ranar Laraba.

David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin bana

Zaman ya gudana ne a harabar tsohon gidan gwamnatin jihar.

Hon. Nanloong Daniel, wanda ke wakiltar mazaɓar Mikang wanda kuma tsohon jagoran masu rinjaye ne a majalisar ta tara, ya samu amincewar dukkanin ’yan majalisar 24 don jagorantar su.

Daniel shi ɗan jam’iyyar APC ne.

Zaɓen nasa ya biyo bayan wani zaman sirri da aka yi tsakanin Gwamna Caleb Mutfwang, tsohon kakakin majalisar Dewan, da sauran ’yan majalisar, domin warware rikicin shugabanci da ke damun majalisar.

Mataimakin akakin ajalisar, Hon. Gwotta Ajang, ne ya jagoranci zaman gaggawar tare da kula da sauyin shugabancin cikin lumana.

Dewan, wanda shi kaɗai ne ɗan jam’iyyar YPP, daga yankin Filato ta Tsakiya, ya ajiye muƙaminsa domin taimakawa wajen kawo ƙarshen rikicin siyasar jihar.

Murabus ɗinsa na zuwa ne bayan wani dogon lokaci aka kwashe ana rikici bayan korar wasu ’yan majalisar jam’iyyar PDP daga majalisar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa
  • Kotu ta ci tarar Natasha N5m saboda kin bin umarninta
  • Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
  • ’Yan Majalisar Wakilai bakwai na Akwa Ibom sun koma APC
  • Baltasar: Mutumin da ya fitar da bidiyon lalatarsa da mata sama da 400 ya gurfana a kotu
  • Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
  • Kotu ta yanke hukuncin rataya ga dalibin da ya kashe malaminsa a Jos
  • ’Yan sanda sun kama matashin da ya kashe mahaifiyarsa a Jigawa
  • Kotu A Kasar Iraki Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wadanda Suka Kashe Ayatullahi Baqir Sadr