Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Published: 4th, July 2025 GMT
A ɓangare guda kuma, kotu ta samu Natasha Akpoti-Uduaghan da laifin saɓawa umarnin kotu ta hanyar rubutun zaulaya da ta yi a shafinta na Facebook a ranar 7 ga watan Aprilu, inda take bayar da haƙuri amma ta hanyar zaulaya ga shugaban majalisar dattawa, Godswill Alpabio.
Kotun ta ce rubutun cin fuska ne ga umarninta, sannan ta umarci Natsha da ta rubuta saƙon bayar da haƙuri a shafukan jarida guda biyu da shafinta na Facebook.
Har ila yau, kotun ta ci tarar Natsha naira miliyan biyar bisa rubutun da ta wallafa a shafin na ta na Facebook.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Majalisar Dattawa Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Dokokin Filato ta zaɓi sabon shugaba
Majalisar Dokokin Jihar Filato ta zaɓi Nanloong Daniel a matsayin sabon Kakakin Majalisar, bayan da Gabriel Dewan ya yi murabus.
Zaɓen sabon kakakin ya gudana ne a wani zaman gaggawa da majalisar ta gudanar ranar Laraba.
David Mark ya fice daga PDP, ya shiga haɗaka don ƙalubalantar Tinubu Najeriya ta kammala dawo da alhazan da suka yi Aikin Hajjin banaZaman ya gudana ne a harabar tsohon gidan gwamnatin jihar.
Hon. Nanloong Daniel, wanda ke wakiltar mazaɓar Mikang wanda kuma tsohon jagoran masu rinjaye ne a majalisar ta tara, ya samu amincewar dukkanin ’yan majalisar 24 don jagorantar su.
Daniel shi ɗan jam’iyyar APC ne.
Zaɓen nasa ya biyo bayan wani zaman sirri da aka yi tsakanin Gwamna Caleb Mutfwang, tsohon kakakin majalisar Dewan, da sauran ’yan majalisar, domin warware rikicin shugabanci da ke damun majalisar.
Mataimakin akakin ajalisar, Hon. Gwotta Ajang, ne ya jagoranci zaman gaggawar tare da kula da sauyin shugabancin cikin lumana.
Dewan, wanda shi kaɗai ne ɗan jam’iyyar YPP, daga yankin Filato ta Tsakiya, ya ajiye muƙaminsa domin taimakawa wajen kawo ƙarshen rikicin siyasar jihar.
Murabus ɗinsa na zuwa ne bayan wani dogon lokaci aka kwashe ana rikici bayan korar wasu ’yan majalisar jam’iyyar PDP daga majalisar.