An cimma matsaya kan dakatar da haska fina-finai 22 a Kano
Published: 20th, May 2025 GMT
Hukumar Tace Fina-finai ta Jihar Kano da masu shirya fina-finai sun cimma matsaya bayan dakatar da wasu fina-finai 22 da suka haɗa da Labarina da Dadin Kowa, Manyan Maga da Garwashi.
An bai wa masu shirya fina-finan wa’adin mako guda daga Litinin 19 zuwa Lahadi 25 ga watan Mayu 2025 domin miƙa fina-finansu don tantancewa da sahalewa.
Wannan na zuwa ne bayan wani taro da aka gudanar tsakanin hukumar da shugabannin masana’antar Kannywood a ranar Litinin.
Shugaban hukumar, Alhaji Abba El-Mustapha, ya ce za a duba fina-finan cikin gaskiya da adalci.
Shugaban MOPPAN reshen Kano, Ado Ahmad Gidan Dabino, ya buƙaci mambobin ƙungiyar da su gaggauta miƙa fina-finansu.
A baya, masu shirya fina-finai sun koka cewa ba a basu damar tantance fina-finan kafin dakatarwa.
Hukumar tace fina-finai ta ce matakin na da nufin tsaftace harkar fina-finai a Jihar Kano.
Idan ba a manta ba a ranar Litinin ne hukumar da dakatar da haska wasu fina-finai gidajen talabijin da YouTube har sai an tantance su.
Fina-finan da hukumar da ta dakatar tun da farko, sun haɗa da Labarina, Dadin Kowa, Manyan Mata, Garwashi, Jamilun Jidda, da Gidan Sarauta.
Sauran sun haɗa da Dakin Amarya, Mashahuri, Wasiyya, Tawakkaltu, Mijina, Wani Zamani, Mallaka, Kudin Ruwa, Boka Ko Malam, Wayasan Gobe, Rana Dubu, Fatake, Shahadar Nabila, Kishiyata da kuma Rigar Aro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Dadin Kowa Garwashi kannywood Labarina Manyan Mata
এছাড়াও পড়ুন:
Sarayal Kuds Ta Kai Wa Matsugunin ‘Yan Mamaya Na Sydriot Hari Da Makamai Masu Linzami
Rundunar Sarayar Kudus dake karkashin kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da kai wa matsugunin ‘yan share wuri zauna na Sydriot hari da makamai masu linzami da su ka yi sanadiyyar kashe da jikkata sojojin mamaya.
Su kuwa kafafen watsa labarun HKI sun samar da cewa, an tsinkayo harba makamai masu linzami guda 3 daga Gaza zuwa Sydriot.
A gefe daya dakarun “Kassam” na kungiyar Hamas sun sanar da cewa sun kai wasu hare-haren da makamai masu linzami zuwa yankin Q20 a sansanin ‘yan share wuri zauna na ” Nir-Ishaq” da “Miftahim.
Bugu da kari dakarun na “Sarayal-Kuds’ sun sanar da kai wa tankar yaki samfurin Mirkava hari ta hanyar wata nakiya mai karfi akan hanyar Zannah,dake gabashin unguwar Shuja’iyyah a birnin Gaza.
Abinda ya biyo baya shi ne kai wani harin da “Sarayal-Kuds’ ta yi akan sojojin mamaya da suke cikin wani gida, ta hanyar amfani da makamin TBG. Da dama daga cikin sojojin mamayar sun halaka da kuma jikkata.
A ranar Talatar da ta gabata ma dai dakarun “Sarayal-Kuds” sun kai wasu hare-haren na hadin gwiwa da ‘ Kassam’ akan cincirindon sojojin mamaya a arewacin Khan-Yunus.