Gwamnatin HKI ta bude kofofin shigar kayakin Agaji zuwa cikin zirin Gaza bayan takurawan kasashen duniya daga ciki har da kawayen ta kan cewa ba zasu iya ci gaba da ganin Falasdinawa suna mutuwa saboda da yunwa ba.

Tashar talabijin ta Almayadeen ta nakalto wata majiyar jami’an gwamnatin HKI na fada a yau litinin kan cewa zasu fara barin kayakin agaji su shiga zirin Gaza daga yau zuwa shawarar da zasu dauka nan gaba.

Labarin ya kara da cewa a safiyar yau litinin tawagar motoci dauke da kayakin abinci da magungun sun shiga zirin gaza ta kofar Karim Abusaleh, sannan MDD zata kula da shigowar kayakin agaji zuwa zirin na Gaza, a fadin tashar radiyo ta sojojin HKI.

Wasu majiyoyin HKI sun bayyana cewa shugaban kasar Amurka Donal Trump ya takurawa firai Ministan HKI kan ya bar abinci ya shiga Gaza amma bai yi masa magana a kan dakatar da budewa juna wuta ba. Hakama wasu kasashen turai sun yi baraza ga Natanyaho kan wannan al-amarin.

A halin yanzu dai masu tsatsauran ra’ayi a gwamnatin HKI suna bada shawarori daban-daban don rama kungiyar Hamas da makamanta ko kuma kwace ikon Gaza  daga hannunta. Wasu sun bada shawara kan cewa kasar Masar ta karbi iko da Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota

Magoya bayan Liverpool da masoya ƙwallon ƙafa a faɗin duniya na cikin jimami bayan ɗan wasan Portugal, Diogo Jota, ya rasu a wani hatsarin mota.

Hatsarin ya auku ne da safiyar ranar Alhamis a yankin Zamora na ƙasar Spain.

’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara NAJERIYA A YAU: Ɓoyayyun Ƙalubalen Da Sabuwar Haɗakar ADC Za Ta Iya Fuskanta

Jota ya rasu yana da shekara 28 a duniha.

Hatsarin ya faru ne a hanyar A-52, kusa da garin Palacios de Sanabria.

Jota yana cikin motar tare da ɗan uwansa, André Silva, wanda shi ma ya rasu.

Silva ɗan wasa ne da ke taka leda a ƙungiyar ƙwallon kafa ta Penafiel a ƙasar Portugal.

Rahotanni sun ce motar ta ƙwace ne tare da barin hanya sannan kuma ta kama da wuta.

Jami’an agaji da ma’aikatan kashe gobara daga Rionegro del Puente sun isa wajen cikin gaggawa, amma ba su iya ceto rayuwar mutanen da ke cikin motar ba.

Hukumomi har yanzu suna bincike don gano musabbabin aukuwar hatsarin.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Antonio Guterres Ya Kadu Saboda Mummunan Halin Da Falasdinawan Gaza Suke Ciki
  • Ambaliya da iska sun rushe gidaje 171 a watanni biyu a Gombe – SEMA
  • Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • Falasdinawa Kimani 40,000 HKI Ta Kora Daga Yankin Yamma Da Kogin Jordan
  • Ɗan wasan Liverpool, Diogo Jota, ya mutu a hatsarin mota
  • Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
  • Yawan Kudin Shiga Da Sin Ta Samu A Fannin Sana’ar Manhaja A Watanni 5 Na Farko Na Bana Ya Wuce Yuan Triliyan 5.5
  • Amurka Ta Dakatar Da Tura Makamai Zuwa Kasar Ukraine Saboda Kada A Sami Karancinsu A Gida
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza