Isra’ila Ta Kai Hari Ga Rumbun Magungunna A Kudancin Gaza
Published: 19th, May 2025 GMT
Hukumar da ke bayar da agajin magungunna ga Falasɗinawa ta ƙasar Birtaniya ta ce Isra’ila ta kai wani hari da ya afkawa rumbun ajiyar magungunna na Asibitin Nasser da ke yankin Khan Younis a tsakar daren da ya gabata a kudancin Gaza .
Hukumar ta ce harin ya auku ne “lokacin da ake kwashe Falasɗinawan da aka kashe da waɗanda aka jikkata zuwa asibiti, bayan wasu jerin hare-haren da Isra’ila ke kai”.
Daga cikin magungunnan da harin ya lalata sun haɗa da waɗanda hukumar ta samar wa asibitin na Nasser. “A yanzu dai muna kallo dukan magungunna da muka bayar tallafi sun ƙone ƙurmus” in ji kakakin hukumar.
Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta fitar da hotunan wuraren da harin ya shafa. Kafar yaɗa labaran Falasɗinawa ta bayar da rahoannin cewa hare-haren da aka kai a birnin sun yi sanadiyyar mutuwar gomman mutane.
Rundunar sojojin saman Isra’ila ta fitar da wata sanarwa cewa a cikin kwana guda kaɗai ta kai hare-hare har 160 a wurare daban-daban da ta ke hara.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato
Mataimakinsa kan harkokin majalisa Honarabul Attahiru Danmadi ne ya wakilci dan majalisar ya kuma tabbatarwa wadanda lamarin ya shafa kokarinsa kan daukar matakan da suka kamata domin tabbatar da tsaron rayukan su da dawowa da zaman lafiya a yankunan.
Garuruwan da ‘yan bindigar suka tarwatsa a gundumar Kuchi sun hada da Fakku, sha’alwashi, tulluwa da Rafin- gora a inda mutane bakwai suka rasa rai. A gundumar Jabo kuwa kauyukan da lamarin ya shafa su ne; Gesolodi, Hilya, Guraye, Guma, Chakai, Modo, Badariya, Tafki, Balera, Gudumawa da Rafin shinka.
“Mun girgiza kwarai da wannan halin da kuke ciki. A matsayina na wakilin ku, zan ci-gaba da kokarin da ya kamata a majalisa domin ganin jami’an tsaro sun kawo karshen wannan ta’addancin.”
Dan Majalisar ya ce ya gabatar da bukata ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa domin tallafawa wadanda lamarin ya shafa kuma zai ci- gaba da bibiya domin ganin tallafin ya samu cikin lokaci.
Ya ce yana kokarin ganin rundunar sojoji ta kara tura wadatattun jami’ai tare da tallafa masu domin yakar ‘yan ta’addan da wanzar da zaman lafiya a yankunan.
Tallafin kayan abinci na gaggawa da dan majalisar ya bayar sun hada da buhuhuwan masara, gero, garin kwaki da kuma kuli- kuli.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp