Hukumar da ke bayar da agajin magungunna ga Falasɗinawa ta ƙasar Birtaniya ta ce Isra’ila ta kai wani hari da ya afkawa rumbun ajiyar magungunna na Asibitin Nasser da ke yankin Khan Younis a tsakar daren da ya gabata a kudancin Gaza .

 

Hukumar ta ce harin ya auku ne “lokacin da ake kwashe Falasɗinawan da aka kashe da waɗanda aka jikkata zuwa asibiti, bayan wasu jerin hare-haren da Isra’ila ke kai”.

 

Daga cikin magungunnan da harin ya lalata sun haɗa da waɗanda hukumar ta samar wa asibitin na Nasser. “A yanzu dai muna kallo dukan magungunna da muka bayar tallafi sun ƙone ƙurmus” in ji kakakin hukumar.

 

Ma’aikatar lafiya ta Gaza ta fitar da hotunan wuraren da harin ya shafa. Kafar yaɗa labaran Falasɗinawa ta bayar da rahoannin cewa hare-haren da aka kai a birnin sun yi sanadiyyar mutuwar gomman mutane.

 

Rundunar sojojin saman Isra’ila ta fitar da wata sanarwa cewa a cikin kwana guda kaɗai ta kai hare-hare har 160 a wurare daban-daban da ta ke hara.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya

Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta bude kofofin wuta a kan haramtacciyar kasar Isra’ila ta hanyar mayar da martani kan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasarta

Iran ta bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya a matsayin mayar da martani ga mummunan zaluncin da suka kaddamar kan lardunan Iran da dama, wanda ya yi sanadiyyar shahadan mutane da dama da jikkata.

Bayan da Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada cewa: Wajibi ne gwamnatin mamayar Isra’ila ta jira mummunan hukunci mai tsanani da kuma makoma mai daci kan abin da aikata, kuma bayan da sabon kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci Manjo Janar Muhammad Pakpour ya bayyana cewa: Sojojin kasar Iran za su bude kofofin jahannama kan kisan yara kanana, Iran ta fara kaddamar da hare-haren daukan fansa mai suna “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda ta harba makamai masu linzami na ballistic da hypersonic kan yankuna daban daban na haramtacciyar kasar Isra’ila.

A cewar faifan bidiyo da aka wallafa, hakika Iran ta kai hare-hare da makamai masu linzami kan tsakiyar birnin Tel Aviv da kuma cibiyoyi da dama na soji da sansanonin sojin saman haramtacciyar kasar Isra’ila.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar
  • Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
  • Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
  • Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
  • Isra’ila ta hana ayarin motocin agaji na arewacin Afrika shiga Gaza
  • An kashe mutum 41 cikin mako ɗaya a Filato