Leadership News Hausa:
2025-05-19@18:52:24 GMT

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara

Published: 19th, May 2025 GMT

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutum 3, Sun Sace 26 A Zamfara

Akalla mutane uku ne aka ce an kashe tare da yin garkuwa da wasu 26 a wani sabon harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a karamar hukumar Kauran Namoda da ke jihar Zamfara. Daily trust ta bankado cewa, hare-haren na tun ranakun Alhamis zuwa Asabar, sun shafi al’ummomi da dama a yankin. Tattalin Arzikin Sin Ya Bunkasa Bisa Daidaito A Afirilu Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe Shaidun gani da ido sun bayyana cewa, lamarin ya fi kamari akauyen Sabon Gari, inda aka kashe mace guda tare da yin garkuwa da mazauna yankin kusan 20.

Wani mazaunin Kauran Namoda, wanda ya bukaci a sakaya sunansa, ya yi ikirarin cewa, adadin ya zarta haka, inda ya ce an kashe mutane hudu – ciki har da mace guda, tare da sace wasu 26. Rahotanni sun ce daga cikin wadanda aka sacen har da wani mutum, da matansa biyu, da ‘ya’yansu uku. An kai hare-haren ne da sanyin safiyar ranar Asabar da misalin karfe 1:00 na dare zuwa 2:30 na daren, duk da kasancewar jami’an tsaro a garin Kaura Namoda. Majiyoyi sun yi zargin cewa, ‘yan bindigar yaran wani fitaccen shugaban ‘yan bindiga, Bello Kaura ne, wanda aka fi sani da Dan Sade, wanda ake alakanta shi da kai hare-haren ta’addanci da dama a fadin kananan hukumomin Kaura Namoda, Bungudu, da Maradun.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato

Aƙalla mutane bakwai sun mutu yayin da wasu 11 suka jikkata a wani hatsarin mota da ya faru a ƙauyen Essa da ke kan hanyar Agaie-Badeggi, ƙaramar hukumar Katcha, jihar Neja.

Binciken LEADERSHIP ya nuna cewa motar ɗauke da hatsi ta gwamnatin tarayya ce, kuma fasinjojinta maza ne kimanin 36, daga Legas zuwa Kano.

Sojoji Sun Harbe Mutane Biyu Har Lahira Da Ake Zargi Ɓarayin Mota Ne A Filato  An Tsinci Gawarwakin Yara Biyar Cikin Tsohuwar Mota A Nasarawa

Hatsarin ya faru ne da ƙarfe 3 na daren ranar Lahadi, lokacin da direban ya yi ƙoƙarin ƙetare wani ɓangare mara kyau na hanyar da ake ginawa.

Daraktan hukumar kula da sufuri na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa ana kan aikin ceto da binciken kan iftila’in.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 3, sun sace 26 a ƙauyukan Zamfara
  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 15 Sun Raunata 3 A Jihar Kebbi
  • Boko Haram ta kashe manoma 90 a Borno cikin wata 5
  • Sojoji Sun Kashe Na Hannun Daman Bello Turji A Sokoto
  • Yanzu-Yanzu: Ana Zargin Makiyaya Sun Kashe Mutane 15 A Benuwe
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas