HausaTv:
2025-07-04@01:40:17 GMT

Falasdinu : ‘Yan jarida 222 aka kashe tun fara yakin Gaza

Published: 19th, May 2025 GMT

Bayanai daga falasdinu na cewa an kashe ‘yan jarida 5 na Falasdinawa a wasu hare-hare daban-daban da Isra’ila ta kai a zirin Gaza, lamarin da ya kai adadin ma’aikatan yada labaran da aka kashe tun farkon yakin Isra’ila a zirin Gaza zuwa 222.

Daga cikin wadanda harin ya rutsa da su har da dan jarida mai daukar hoto Aziz al-Hajjar, da matarsa, da ‘ya’yansu, wadanda aka kashe a ranar Lahadi, lokacin da jiragen yakin Isra’ila suka kai hari a gidansu da ke unguwar Saftawi a arewacin Gaza.

A gefe guda kuma, an kashe dan jarida Ahmad al-Zinati tare da matarsa, Nour al-Madhoun, da ‘ya’yansu, Mohammad da Khaled, a lokacin da aka kai wa tantin su hari a Khan Younis a yammacin ranar Asabar.

Shahadar wadannan ‘yan jarida na zuwa ne kwanaki biyu kacal bayan mutuwar Ahmed al-Halou, wani dan jarida da ke aiki da kafar yada labaran birnin Quds, wanda aka kashe a wani harin da Isra’ila ta kai a zirin Gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato

Wasu ‘yan bindigar da ake zargi Lukurawa ne a wani sabon hari sun kashe mutane sama da 15 a Qaramar Hukumar Tangaza ta jihar Sakkwato, ranar Litinin da ta gabata.

Babban Jami’i a Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Qasa(Red Cross) reshen Sakkwato Alhaji Abubakar Ainu ya tabbatar wa Aminiya harin wanda ya yi matuqar tayar da hankalin mutanen yankin ganin an xauki dogon lokaci kafin kawo irin wannan hari mai muni.

Ainu ya ce, “jami’anmu na sa kai sun ziyarci qauyen Kwalajiya na mazabar Magoho a garin Tangaza domin jajantawa da kuma halartar sallah janaza ta muanen da ‘yan bindigar suka kashe sama da 15.  Waxanda suka jikkata an kai su Asibitin Kashi na Wamakko da Asibitin Koyarwa ta Xanfodiyo da na Qwararru a birnin jiha domin karvar magani.”

Ya ce yankin na cikin wuraren da ke fama da matsalar tsaro ta varayin shanu da masu tayar da qayar baya.

“Wannan lamari baya da daxi ko kaxan, dubi yadda aka mayar da wasu mata zawarawa aka mayar da wasu yara marayu domin biyan wata buqata wadda addini bai yarda da ita ba, ina kira ga hukuma ta sake salon yaqar ‘yan bindiga da take yi,” in ji Ainu.

Wani mazauni qauyen Kwalajiya ya ce ‘yan bindigar Lukurawa sun zo a qauyen a daren Lahadi har zuwa Asuba ta ranar Litinin in da suka kashe wasu mutane a harin da suka kai, a lokacin da suka yi ta harbi kan mai uwa da wabi.

“Bayan sun kashe mana mutane sun tafi da dabbobi masu yawa, duk da mutanenmu sun yi qoqari amma yawan mutane da makaman da suke xauke da su ya sa suka fi qarfinmu. Har zuwa yanzu ba mu san adadin waxanda aka kai asibiti ba domin suna da yawa, sai dai waxanda suka rasu 15 muka yi wa Sallah.

“Muna kira ga jami’an tsaro su mayar da hankali wurin korar mana waxannan ‘yan bindigar don mu samu zaman lafiya a jiha baki xaya.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar Tinubu – Amaechi
  • ’Yan Najeriya sun fara begen Buhari saboda azabar TIinubu – Amaechi
  • Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya
  • Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • Za a fara cin tarar masu shigar banza N50,000 a Delta
  • Wakilan Kasashen Duniya Da Kungiyoyin Sun Je Ta’aziyya Mutanen Da Suka Yi Shahada A Yakin Iran Da H.K.Isra’ila
  • Isra’ila na bincike kan harin dakarunta da ya kashe fararen hula a Gaza
  • Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara