HausaTv:
2025-05-01@03:56:48 GMT

Amurka Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen Don Tallafawa HKI

Published: 20th, March 2025 GMT

Sojojin Amurka sun kai sabbin hare–hare kan kasar Yemen a safiyar yau Alhamis inda suka lalata gine-gine a garuriwa Al-Hudaida da kuma  Sa’ada.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban kasar Amurka Donal Trump kafin haka ya na fadar cewa, sai ya shafe kungiyar Ansarullah wacce take iko da kasar Yemen daga doron kasa.

Tun ranar Asabar da ta gabata ce sojojin Amurka da Burtaniya wadanda suke da jiragen yakinsu a cikin tekun maliya da wasu wurare a yakin suka fara kaiwa kungiyar hare-hare saboda goyon bayan ga HKI.

Kafin haka dai kungiyar Ansarullahi ta bawa HKI kwanaki huda ta kawo karshen kofar ragon da ta yiwa falasdinawa kimani miliyon biyu a gaza, inda suka hana shigowar abinci da abin sha shiga cikin yankin.

A lokacinda wa’adin ya cika ne HKI ba ta amsa kiran kungiyar ba, sai ta dauki matakin hana jiragen ruwan HKI da wadanda suke zuwa can wucewa ta tekun maliya.

Amurka ta shiga yakin ne da sunan hana kungiyar Ansarallah hana zirga-zirgan jiragen ruwan kasuwanci a tekun maliya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae

Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae, a karon farko da yayi magana dangane da fashewar tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae ya gabatar da Ta’ziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu ko suka jikata a wannan hatsarin. Ya kuma bukaci a gudanar da bincike mai mai zurfi don gano musabbabin fashewar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jagoran yana bada umurni ga ma’aikatar shari’aa a kasar ta gudanar da cikekken bincike don sanin abinda ya faru saboda daukar matakan da suka dace don hana irin wannan sake faruwa nan gaba, sannan idan akwai wadanda suka yi kuskure a hukunta su.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gobarar da ta taso a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajae, daya daga cikin tashoshin jirage masu muhimmanci  a tattalin arzikin kasar, don haka dole ne a kara daukar matakan tsaro da amincin tashar don hana irin wannan sake faruwa.

Sanadiyyar wannan hatsarin majalisar dokokin kasar ta shelanta makoki a duk fadin kasar a yau Litinin. Sannan shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan ya ziyarci tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae don ganewa idanunsa abubuwan da suka faru da kuma barnan da aka tabka.

Ya zuwa yanzun wadanda suka rasa rayukansu sun kai 40 sannan wadanda suka rasa rayukansu sun kai dubu guda.  

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Munafunci Dodo Ya Kan Ci Mai Shi
  • Katafaren Jirgin Daukar Jiragen Yaki Na Kasar Amurka Harry Truman Zai Fice Daga Tekun Maliya
  • ISWAP ta ɗauki alhakin kashe mutum 26 a Borno
  • Sabbin Bayanai Kan Fashe-Fashe Wasu Abubuwa A Tashar Jiragen Ruwan Kasar Iran
  • Wani abin fashewa ya kashe mutum 26 a Borno
  • Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
  • Shugaban Kungiyar Hizbullah Ya Abbaci Abubuwa 3 Wadanda Yakamata Kasar Ta Maida Hankali A Kansu
  • Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Sa’o’ii 72
  • Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
  • Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen