HausaTv:
2025-06-15@09:41:12 GMT

Amurka Ta Kai Sabbin Hare-Hare Kan Kasar Yemen Don Tallafawa HKI

Published: 20th, March 2025 GMT

Sojojin Amurka sun kai sabbin hare–hare kan kasar Yemen a safiyar yau Alhamis inda suka lalata gine-gine a garuriwa Al-Hudaida da kuma  Sa’ada.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban kasar Amurka Donal Trump kafin haka ya na fadar cewa, sai ya shafe kungiyar Ansarullah wacce take iko da kasar Yemen daga doron kasa.

Tun ranar Asabar da ta gabata ce sojojin Amurka da Burtaniya wadanda suke da jiragen yakinsu a cikin tekun maliya da wasu wurare a yakin suka fara kaiwa kungiyar hare-hare saboda goyon bayan ga HKI.

Kafin haka dai kungiyar Ansarullahi ta bawa HKI kwanaki huda ta kawo karshen kofar ragon da ta yiwa falasdinawa kimani miliyon biyu a gaza, inda suka hana shigowar abinci da abin sha shiga cikin yankin.

A lokacinda wa’adin ya cika ne HKI ba ta amsa kiran kungiyar ba, sai ta dauki matakin hana jiragen ruwan HKI da wadanda suke zuwa can wucewa ta tekun maliya.

Amurka ta shiga yakin ne da sunan hana kungiyar Ansarallah hana zirga-zirgan jiragen ruwan kasuwanci a tekun maliya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila

Dakarun kare juyin juya halin Musulunci (IRGC) sun kaddamar da wani sabon harin makamai masu linzami da jirage marasa matuka kan Isra’ila a cikin daren jiya Asabar, biyo bayan matakin farko na harin ramuwar gayya na kan harin Isra’ila na ranar Juma’a.

Jim kadan bayan harba makamai masu linzami da jirage marasa matuka, sashen hulda da jama’a na IRGC ya ba da sanarwar kaddamar da wani sabon shiri na manyan makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuka.

Sanarwar ta yi nuni da cewa, sashen kula da sararin samaniya na IRGC ya fara wannan sabon mataki na aikin a matsayin mayar da martani kai tsaye ga sabbin ta’addancin gwamnatin sahyoniyawan.

Babban abin da aka fi mayar da hankali kan wannan sabon farmakin na ‘Operation True Promise III’ an bayar da rahoton cewa, birnin Haifa mai tashar jiragen ruwa ya kunshi muhimman wuraren soji da masana’antu na gwamnatin.

Hare-haren sun shafi wasu muhimman cibiyoyin soji da masana’antu na Isra’ila, da suka hada da matatun mai da na wutar lantarki a Haifa, inda aka ce gobara ta tashi a sanadiyar haka.

Daya daga cikin faifan bidiyon ya nuna wata gagarumar gobara da ta tashi a matatar mai ta Haifa bisa tasirin da manyan makamai masu linzami na Iran suka yi, wanda ya haskaka sararin samaniyar yankunan da aka mamaye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran ta sake kai hare-haren martani kan Isra’ila
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Sin Ta Yi Kira Ga Isra’ila Da Ta Dakatar Da Kaddamar Da Hare-hare Kan Iran
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Bude Kofofin Jahannama Ga Yahudawan Sahayoniyya
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Iran : harin da Isra’ila ta kai ‘ ayyana yaki’ ne_ Araghchi
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
  • Kamfanonin Waje Sun Ce Dole Ne Su Shiga A Dama Da Su A Cikin Kasuwar Kasar Sin
  •   Bokoharam Ta Kashe Sojojin Kamaru Ta Hanyar Amfani Da Jirgin Sama Maras Matuki