Alakar tattalin arziki da cinikayya bisa daidaito da aminci kuma mai dorewa tsakanin Sin da Amurka ta dace da muhimman muradun kasashen biyu, kuma za ta amfanar da kamfanoni a duk duniya, a cewar mataimakin ministan cinikayya Wang Shouwen yayin wata ganawa da Ramon Laguarta, shugaban kamfanin PepsiCo a ranar Talata.

Da yake karin haske kan yadda kasar Sin ke da karfin gwiwar cimma burinta na bunkasa tattalin arzikinta na shekarar 2025 da aka gabatar a cikin rahoton aikin gwamnati, Wang, kuma wakilin harkokin cinikayya na kasa da kasa na kasar Sin, ya bayyana cewa, wasu jerin tsare-tsare da kasar ta bullo da su na fadada bukatun cikin gida, da sa kaimi ga inganta tsare-tsaren yin sayayya za su samar da karin damammaki ga kamfanonin masu jarin waje, ciki har da PepsiCo. (Mai fassara: Mohammed Yahaya)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho

Karuwar tasirin da kasar Sin ke yi a fagen ci gaban kimiyya da fasaha a duniya ba barazana ba ce, sai dai wata dama ce ta kawo ci gaba mai gamewa. Diamond ya kara da cewa, “Kasancewar na yi aiki kafada da kafada da wasu jami’o’i da cibiyoyin kasar Sin na tsawon shekaru masu yawa, na yi amanna da yadda kasar Sin ta dukufa ga samar da kimiyya da fasaha mai bude kofa ga duk duniya bisa adalci.”

Kazalika, masanin kimiyya, mamba a makarantar nazarin kimiyya da fasaha ta Afirka, Farfesa Felix Dapare Dakora, ya nuna yadda kasar Sin ke karfafa shigar kasashe masu tasowa cikin harkokin kimiyya a duniya. Yana mai cewa, “A halin yanzu, an gode da samuwar shirye-shiryen da kasar Sin ke mara musu baya a karkashin dandaloli kamar BRI, inda masana kimiyya daga kasashe masu tasowa ke samun damammakin da ba a taba ganin irinsu ba domin bayar da gudummawa da kuma zama a kan gaba.”

Jagorancin da kasar Sin ke yi wajen karfafa hadin gwiwa da kasashe masu tasowa ya bai wa kasashen damar fahimtar cewa lallai hadin kai shi ne karfin da ake bukata, kuma ana iya magance galibin matsalolin da suka zama karfen kafa sakamakon matakan masu shamakancewa, tare da tabbatar da cewa ba a bar kowace kasa a baya ba.

A kullum dai, mai burin ganin ci gaban wasu ba zai taba rasawa ba, kana mai tsoron ta-mutu kuma, zai ci gaba da yin maho! (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • “Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • Mu’ammalar Al’adu Muhimmin Karfi Ne Na Ciyar Da Bunkasar Wayewar Kan Bil’adama Da Wanzar Da Zaman Lafiyar Duniya
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki
  • Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
  • An Bude Taron Ministoci Kan Wayewar Kai A Birnin Beijing
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista
  • An Yi Hasashen Karuwar Tattalin Arzikin Kasar Sin Za Ta Zarce Yuan Tiriliyan 35 Tsakanin 2021 Zuwa 2025
  • Mai Tsoron Ta Mutu, Shi Yake Maho
  • Akwai Bukatar Sin Da Masar Su Zurfafa Hadin Gwiwa Domin Kare Muradunsu