Harin da Isra’ila ta kai ya kashe Falasdinawa 9 a arewacin Gaza
Published: 15th, March 2025 GMT
Rahotannin dake fitowa daga Falasdinu na cewa wani hari da Isra’ila ta kai a arewacin zirin Gaza ya kashe akalla Falasdinawa tara, ciki har da ‘yan jarida uku a cikin gida, in ji ma’aikatan lafiya.
An kai harin ta sama a wata mota a garin Beit Lahiya da ke arewacin zirin yau Asabar.
A cewar likitocin, mutane da dama sun samu munanan raunuka, tare da jikkata a ciki da wajen motar.
“An kai shahidai tara zuwa asibiti, da suka hada da ‘yan jarida da dama da ma’aikata daga kungiyar agaji ta Al-Khair, sakamakon harin da aka kai wa motar da wani jirgi mara matuki a garin Beit Lahia, tare da luguden wuta a yankin,” in ji kakakin hukumar tsaron farar hula Mahmoud Bassal.
Shaidu da sauran ‘yan jarida sun ce mutanen da ke cikin motar na wata kungiyar agaji ve a garin, kuma Sun samu rakiyar ‘yan jarida da masu daukar hoto lokacin da harin ya same su.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sakon Jagora : Isra’ila ta jira hukunci mai tsanani bayan hari kan Iran
Bayan harin da gwamnatin Sahayoniya ta kai kasarmu, Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya aike da sako ga al’ummar Iran. Ga sakon kamar haka
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
Al’ummar Iran masu daraja!
Gwamnatin yahudawan sahyoniya ta hanyar aikata wani laifi da sanyin safiyar yau, ta sake bayyana munanan dabi’arta da fasadi.
Ta hanyar kai hari dole ne wannan ya fuskanci hukunci mai tsanani.
A wannan harin makiya, kwamandoji da masana kimiyya da dama sun yi shahada.
Wadanda suka gaje su kuma da abokan aikinsu za su ci gaba da aiki nan take akan wannan tafarki, godiya ta tabbata ga Allah.
Ta hanyar wannan danyen aiki, gwamnatin Sahayoniya ta kaddara akan ta cewa zata fuskanci martini mai radadi.