Aminiya:
2025-07-04@22:00:13 GMT

An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno

Published: 4th, July 2025 GMT

Dakarun rundunar sojin  ‘Operation Haɗin Kai’ sun ce dakarunsu sun kai ga nasarar gano wasu bama-bamai guda 56 da ake zargin mayaƙan ISWAP ne suka binne a kan gadar Marte zuwa Dikwa da ke Jihar Borno.

Sojojin sun kuma daƙile wani harin da ka iya zama wani babban harin da zai haifar da mummunan ɓarnar rayuka da dukiyoyi.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa

Majiyoyin da ke da alaƙa da rundunar ta OPHK  ta tabbatar da a ranar Juma’a cewa, aka gano bama-baman a wani samame da sojojin na runduna ta 24 da ke Dikwa, Jihar Borno suka yi.

A cewar majiyar, ’yan tada ƙayar bayan sun sanya bama-baman ne a kan gadar da dabarar da nufin yin ɓarna mai yawa tare da daƙile zirga-zirgar sojoji da fararen hula a kan hanyar.

Majiyar ta ce, “Sojojin da ke aiki da sahihan bayanan sirri, sun gano na’urorin kafin su tarwatse.

Ya ƙara da cewa, nan take aka tura tawagar da ke kawar da bama-bamai (EOD) zuwa wurin domin taimakawa wajen tabbatar da tsaron na’urorin don kwance su kafin su kaiga tashi.

Hotunan farmakin sun nuna wasu bama-bamai da aka gano a jikin wasu muhimman sassan gadar da ta haɗa manyan garuruwa biyu a Arewacin Borno.

Majiyoyin sun ce saurin shiga tsakani da sojojin suka yi ne ya daƙile wani mummunan harin ta’addanci, wanda ake iya kaiwa jami’an tsaro, al’ummomin farar hula da masu ayyukan jin ƙai a yankin.

Ana ci gaba da sa ido a yankin, yayin da ake ci gaba da aikin share sauran abubuwan fashewa a yankin da zarar an gano su.

Don haka rundunar ta OPHK ke kira ga jama’a musamman masu abubuwan hawa da su riƙa yin taka tsantsan gami da lura akan waɗannan hanyoyin tare da kai rahoton duk wani abu da suke zargi ga jami’an rundunar don magance shi akan lokaci kafin ya kai ga haddasa mummunan lamari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Dikwa ISWAP Marte Operation Haɗin Kai

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran Ta Bayyana Lokacin Ci Gaba Da Ayyukan Cibiyoyinta Ta Nukiliya

Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran ta jaddada cewa: Gudanar da masana’antun nukiliyar kasar za ta ci gaba da kuma fadada bunkasar da suke samu

Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran, Mohammad Islami, dangane da yadda yahudawan sahayoniyya da Amurka suka kai hare-hare kan cibiyoyin nukiliyar Iran, ya jaddada cewa: Masana’antar nukiliya ba wani abu ba ne da za a iya rusa shi ta hanyar jefa masa bam saboda fasahar masana’antar nukiliya irin ta Iran tana bunkasa ce da ilimummukan masana ‘yan asalin kasa da suke da zurfin fasahar ilimin.

Kamfanin dillancin labaran Mehr ya watsa rahoton cewa: Mohammad Islami shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran ya bayyana cewa, bayan wani taron majalisar ministocin kasar da aka gudanar a ranar Laraba, don tattaunawa kan yadda gwamnatin ‘yan sahayoniyya da Amurka suka kai harin wuce gona da iri kan cibiyoyin nukiliyar kasar Iran, cewa: Wannan farmakin da aka kai kan Iran, wani rauni ne ga kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya da kuma nuna cewa dokar daji ta mamaye duniya, kuma wadanda ba su da karfi ba za su iya ci gaba da rayuwarsu ba lamarin da tuni al’ummar Iran suka fahimci hakan da kyau.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • Harin Filato: Remi Tinubu ta ba da gudummawar Naira biliya 1
  • ‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato
  • Hukumar Makamashin Nukiliya Ta Iran Ta Bayyana Lokacin Ci Gaba Da Ayyukan Cibiyoyinta Ta Nukiliya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • ’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe
  • Aragchi: Hare-Haren HKI Ya Kara Rashin Zaman Lafoya A Yankin Yammacin Asiya