’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Published: 4th, July 2025 GMT
A yayin bincike, ’yansanda sun ƙwato motocci huɗu, wuƙa, kayan sojoji, da harsasai.
Game da fashi da makami, rahoton ya nuna cewa an samu rahotannin guda biyar daga watan Mayu zuwa Yuni, kuma an kama mutane 17 da ake zargi da aikata laifin fashin.
Kwamishinan ya kuma ce an samu rahotannin safarar yara guda huɗu, inda aka kama mutane takwas da ake zargi.
A cikin makaman da rundunar ta ƙwato akwai bindigogi AK-47 guda uku, ƙaramar bindiga ƙirar gida guda ɗaya, bindiga ƙirar Baretta, bindiga mai fitar da wuta, bindigogin LAR guda biyu, da harsasai guda 36.
Sauran abubuwan da aka kwato sun haɗa da: gatari guda ɗaya, na’urar sadarwa (walkie-talkie) guda tara, da kuɗi Naira 79,000.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
An kama wata matar aure a garin Kuta, hedikwatar Karamar Hukumar Shiroro ta Jihar Neja, bisa zargin yankar wuyan mijinta, Salisu Suleiman, da wukar girki.
Majiyoyi sun ce matar ta kuma soka wa mijin wuka a idonsa na hagu, lamarin da ya lalata idon gaba ɗaya.
Wata majiya da ta nemi a ɓoye sunanta ta bayyana wa wakilinmu cewa ma’auratan sun samu saɓani ne, inda matar ta jira har sai da mijin ya kwanta barci kafin ta kai masa hari da wuƙa.
Kakakin ’yan sanda na Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya ce lamarinya auku ne da safiyar Asabar, 1 ga Nuwamba, 2025.
A cewarsa, “A ranar 1 ga Nuwamba, da misalin ƙarfe 2:30 na asuba, wani Salisu Suleiman na garin Kuta ya samu saɓani da matarsa, Halima Salisu, inda da mijin ya kwanta barci, matar ta ɗauki wuƙa ta yankar masa wuya, sannan ta soka masa a idon hagu.”
SP Abiodun ya ce an garzaya da wanda abin ya faru da shi Asibitin Gabaɗaya na Kuta, daga nan kuma aka mayar da shi Asibitin Ƙwararru na IBB da ke Minna domin ƙarin kulawar likitoci.
Ya ƙara da cewa, “An kama wadda ake zargi, kuma tana tsare a hannun ’yan sanda domin ci gaba da bincike da kuma gurfanar da ita a gaban kotu.”