Aminiya:
2025-09-18@02:13:19 GMT

Nijar ta kori wasu kamfanonin China 3 daga ƙasar

Published: 15th, March 2025 GMT

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta kori manyan jami’an wasu kamfanonin CNPC da WAPCO da SORAZ na China daga ƙasar.

Haka nan, gwamnatin ta kuma soke lasisin wani babban Otel na China da ke birnin Yamai.

Faɗuwar farashin kayan abinci a watan azumi ta shammace mu – ‘Yan kasuwa ’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina

Gwamnatin Nijar ɗin na zargin kamfanonin da ƙin mutunta dokokin aiki a ƙasar da ma na yarjejeniyar aiki da suka sanya wa hannu.

Wasu majiyoyi na kusa da gwamnatin sun tabbatar da cewa tun a ranar Larabar da ta gabata Shugaba Janar Abdourahmane Tchiani ya bayar da wa’adin sa’o’i 48 ga manyan daraktacin kamfanonin CNPC mai aikin haƙar man fetur a Nijar da na kamfanin WAPCO da ke kula da jigilar ɗanyen man Nijar ta bututu zuwa tashar ruwan Cotonou da kuma na babbar matatar mai ta SORAZ su bar ƙasar baki ɗaya.

Majiyoyi na cewa hukumomin ƙasar ta Nijar na zargin kamfanonin na Chinar da aikata laifuka daban-daban da suka haɗa da ƙin mutunta yarjejniyar horas da ma’aikata ‘yan Nijar.

Haka kuma, hukumomin na zargin ci da gumin ma’aikatan Nijar ta hanyar ba su albashin da bai taka kara ya karya ba a gaban takwarorinsu na Chinar da ma shirya makarkashiyar da ta haddasa matsalar karancin man fetur a baya bayan nan a kasar.

Yanzu haka dai ko baya ga korar waɗannan manyan daraktoci na ƙasar China, gwamnatin mulkin sojan Nijar ta kuma sanar da ƙwace lasisin aiki na babban Hotel na SOLUXE mallakar China da ke birnin Yamai.

A ɓangaren ɗaya kuma Gwamnatin Nijar ɗin ta ba da izinin rufe asusun ajiyar kuɗi na babbar matatar mai ta kasa ta SORAZ.

Kawo yanzu dai kasar ta China ba ce uffan ba, haka kuma mahukuntan kamfanonin da abin ya shafa da aka tuntuɓa ba su magantu a kan lamarin ba.

A shekarar da gabata ce Nijar ta ƙulla yarjejeniyar cefanar da ɗanyen man fetur ta dala miliyan 400 da ake haƙowa a ƙasar.

A yayin da wasu ‘yan Nijar ke yaba wa da matakin wasu na ganinsa a matsayin barazana ga makomar hulɗar ƙasar da China da ma tattalin arzikin Nijar ɗin baki ɗaya.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijar SORAZ WAPCO

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara

Gwamnatin Jigawa ta amince da sabon tsarin ka’idojin aiki domin aiwatar da shirin kula da lafiyar mata masu juna biyu, da jarirai da ƙananan yara kyauta a cibiyoyin lafiya na  jihar.

Kwamishinan Yaɗa Labarai, Alhaji Sagir Musa Ahmed, ya bayyana haka bayan zaman majalisar zartarwa da aka gudanar a gidan gwamnati Dutse.

Ya ce ka’idojin za su taimaka wajen inganta nagartar hidima, fayyace karewar ma’aikata, da kuma tabbatar da gaskiya, da bin doka da tsari a asibitoci.

Kwamishinan ya ƙara da cewa matakin ya dace da manufar gwamnatin jihar na rage mace-macen mata da yara da kuma tabbatar da samun ingantacciyar kulawa ga kowa.

Ya ce za a fara aiwatar da tsarin nan take, tare da horas da shugabannin asibitoci da cibiyoyin lafiya na ƙananan hukumomi domin cimma nasarar shirin .

 

Usman Muhammad Zaria 

 

 

 

Kana so in ƙara ɗan salo na labarin jarida (irin rubutun kafafen yaɗa labarai) ko a barshi haka cikin sauƙin bayani?

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • DAGA LARABA: Dalilan Tashin Farashin Doya A Wasu Kasuwannin Najeriya
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  •  Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa