“ADC za ta fuskanci matsala wajen zaɓen wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa”
Published: 4th, July 2025 GMT
Datti Baba-Ahmed, wanda ya tsaya takarar mataimakin shugaban ƙasa a jam’iyyar LP a zaɓen 2023, ya bayyana cewa ADC za ta fuskanci babban ƙalubale wajen fitar da wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa a 2027.
Sabuwar haɗakar ta haɗa da fitattun ’yan siyasa irin su tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar; ɗan takarar shugaban ƙasa na LP a 2023, Peter Obi.
Sauran sun haɗa da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai da sauran shugabannin jam’iyyun adawa.
Sun ƙaddamar da sabuwar haɗakarsu a ƙarƙashin jam’iyyar ADC a ranar Laraba.
A wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise a ranar Alhamis, Baba-Ahmed, ya ce wannan matakin da ’yan adawar suka ɗauka yana kama da dabarar da Shugaba Tinubu ya yi kafin zaɓen 2015, lokacin da jam’iyyu suka haɗu suka kafa APC.
Amma ya ce akwai bambanci, domin a 2015, mutane da dama sun riga sun ɗauki Muhammadu Buhari a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa tun kafin zaɓen fidda gwani.
Ya ce Tinubu ya goyi bayansa da fatan cewa daga baya zai gaje shi.
Baba-Ahmed ya ce a yanzu, babu wani ɗan takara da aka amince da shi a fili a cikin sabuwar haɗakar.
A cewarsa hakan na iya janyo rikici da gasa mai zafi a lokacin zaɓen fidda gwanin.
“Akwai rashin jituwa a cikin wannan haɗakar. A wancan lokacin, an ɗauki Buhari a matsayin wanda zai yi takara.
“Tinubu ya mara masa baya domin ya san zai zama shugaban ƙasa daga baya. Amma a yanzu, babu wani da aka zaɓa a matsayin ɗan takara.
“Za a samu gasa sosai, kuma wataƙila zaɓen fidda gwani ba zai kasance mai tsafta ba. Tambayar ita ce, me zai faru daga baya?” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Zaɓe takarar shugaban ƙasa
এছাড়াও পড়ুন:
Aragchi Ya Musanta Zargin Da Jamus Take Watsawa Dangane sa Shirin Nukliyar Kasar
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya yi watsi da labarin da ministan harkokin wajen kasar Jamus ya watsa dangane da shirin Nukliyar kasarsa ya kuma kara da cewa labarin jabu ne.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a shafinsa na X . Ya kuma yi watsi da zancen ministan harkokin wajen kasar Jamus wanda yake cewa, jinginar da aiki tare da hukumar makamashin nukliya ta duniya wato IAEA wanda JMI ta yi, ya na nuna cewa ba wanda zai bincika ayyukanta na makamashin nukliya ba, kuma ta rufe kofar tattaunawa Kenan.
Aragchi ya bayyana cewa wannan ba haka bane, saboda shirin nukliyar kasar Iran a halin yanzu ya na karkashin majalisar koli ta tsaron kasar Iran ne, don haka ita ce zata fayyece yadda huldar shirin zai kasance tare da hukumar IAEA. Sannan Iran bata fice daga yarjeniyar NPT ba.
Kasar Jamus dai tana goyon bayan hare=hare da HKI da AMurka suka kaiwa JMI a yakin kwanaki 12, dagan cikin harda hare-hare kan cibiyoyin makamashin nukliyar kasar. Ya ce aiki ne da bai dace ba wacce JKI ta yi madadin kasashen yamma.