Datti Baba-Ahmed, wanda ya tsaya takarar mataimakin shugaban ƙasa a jam’iyyar LP a zaɓen 2023, ya bayyana cewa ADC za ta fuskanci babban ƙalubale wajen fitar da wanda zai yi mata takarar shugaban ƙasa a 2027.

Sabuwar haɗakar ta haɗa da fitattun ’yan siyasa irin su tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar; ɗan takarar shugaban ƙasa na LP a 2023, Peter Obi.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa

Sauran sun haɗa da tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai da sauran shugabannin jam’iyyun adawa.

Sun ƙaddamar da sabuwar haɗakarsu a ƙarƙashin jam’iyyar ADC a ranar Laraba.

A wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise a ranar Alhamis, Baba-Ahmed, ya ce wannan matakin da ’yan adawar suka ɗauka yana kama da dabarar da Shugaba Tinubu ya yi kafin zaɓen 2015, lokacin da jam’iyyu suka haɗu suka kafa APC.

Amma ya ce akwai bambanci, domin a 2015, mutane da dama sun riga sun ɗauki Muhammadu Buhari a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa tun kafin zaɓen fidda gwani.

Ya ce Tinubu ya goyi bayansa da fatan cewa daga baya zai gaje shi.

Baba-Ahmed ya ce a yanzu, babu wani ɗan takara da aka amince da shi a fili a cikin sabuwar haɗakar.

A cewarsa hakan na iya janyo rikici da gasa mai zafi a lokacin zaɓen fidda gwanin.

“Akwai rashin jituwa a cikin wannan haɗakar. A wancan lokacin, an ɗauki Buhari a matsayin wanda zai yi takara.

“Tinubu ya mara masa baya domin ya san zai zama shugaban ƙasa daga baya. Amma a yanzu, babu wani da aka zaɓa a matsayin ɗan takara.

“Za a samu gasa sosai, kuma wataƙila zaɓen fidda gwani ba zai kasance mai tsafta ba. Tambayar ita ce, me zai faru daga baya?” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Zaɓe takarar shugaban ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista

“Shekaru goma da suka wuce, gudummawar da ma’adanai ke bayarwa ga GDP na kasarmu bai wuce 0.5% ba, amma a yau ya karu zuwa 1.8% – alkalumman NBS suka nuna a cikin rabi na biyu na 2025 wanda ba a taba ganin irinsa ba”.

 

Da yake tsokaci kan ci gaban fannin, Ministan ya bayyana cewa, makon hako ma’adanai na Nijeriya ya yi nuni da yadda masana’antar ke sauya tunani zuwa tsari mai kyau, da sabbin abubuwa, da ke lalubo masu zuba jari na kasa da kasa.

 

Ya bayyana cewa, sauye-sauyen sun tattara ne a kan gaskiya, rage haɗari, da inganta masana’antar.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadin Mutuwar Mutane 236 A Jihohi 27 Da Birnin Tarayya October 13, 2025 Manyan Labarai Ta’addanci: Ana Fuskantar Ƙarancin Man Fetur A Mali Sakamakon Datse Hanyoyin Shiga Bamako October 13, 2025 Labarai Gwamnatin Tarayya Ta Gargaɗi ASUU Kan Yajin Aiki, Ta Ce “Babu Aiki, Babu Albashi” October 12, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa
  • Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu
  • Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani
  • An kama mata da miji suna safarar makamai a Kaduna
  • Al’ummun Kasashe Daban-Daban Sun Yabawa Shawarwarin Sin Dake Taimakawa Wajen Dunkulewa Don Hanzarta Ci Gaban Mata
  • Iran Ta Jadda Cewa A Shirye Take Ta Kare Kanta A Duk Wani Yaki Wanda Makiya Zasu Dora Mata
  • Shugaban Hukumar Zaɓen Yobe Jihar Yobe ya rasu
  • Kamaru: Jam’iyyun adawa sun ayyana Bakary a matsayin wanda ya lashe zaɓe
  • Ba Gudu Ba Ja-da-baya Kan Ci Gaba Da Kwaskwarima Ga Tsarin Haƙar Ma’adanai – Minista
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako