Aminiya:
2025-07-09@05:58:39 GMT

Faɗuwar farashin kayan abinci a watan azumi ta shammace mu – ‘Yan kasuwa

Published: 15th, March 2025 GMT

’Yan kasuwa na ci gaba da neman mafita bayan karyewar farashin kayan masarufi, musamman abinci da ake ci gaba da samu, sabanin yadda aka saba fuskantar tashin gwauron zabon farashi a lokacin azumi a Nijeriya. 

Farashin kayan abincin ya karye ne a lokacin da wasu ’yan kasuwar suka riga suka saye amfanin gona suka boye tun a lokacin kaka, da nufin rubanya kudinsu idan farashinsa ya yi tashin gwauron zabo daga musamman a lokaci irin wannan na azumin watan Ramadan, da wasu bayin Allah suke saya don raba wa mabukata.

’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina ’Yan Nijeriya su ƙara haƙuri kan matakan da muke ɗauka — Tinubu

Kudin hatsi irin su shinkafa da wake da masara da dawa da gero da fulawa da kuma cimaka ’yan kamfani da ake sarrafawa daga fulawa kamar taliya da garin samanbita, duk sun yi kasa.

Wasu majiyoyi sun danganta faduwar farashin da janye haraji kan wasu nau’ukan abincin da ake shigo da su daga kasashen waje da Gwamnatin Tarayya ta yi.

An samu kai a wannan yanayi ne a lokacin da manoma suka riga suka sayar da kusan daukacin amfanin gonar da suka noma da damina ga ’yan kasuwa.

Akwai yiwuwar karin sauki — Dan kasuwa

A zantawarsa da Aminiya kan yadda faduwar farashin ta shammace su, wani mai sayar da kayan abinci a Babbar Kasuwar Garin Kubwa da ke Abuja, Alhaji Almustafa Imam, ya ce al’amarin ya dagula masu lissafi, da za su jima ba su warware ba.

Amma ya ce gara hakan, idan aka kwatanta da yadda suka rika fuskantar hauhawar farashi akai-akai sama da shekara guda da ta gabata, a duk lokacin da suka koma kasuwa don saro kaya.

“A lokacin dole sai mun yi cikon kudi don iya sayen adadin abin da muke saya,” in ji shi.

Ya ce saukar farashin kayan abincin na yanzu ya sa abokan huldarsu na sayan karin kaya a wajensu, sabanin yadda a baya suke rage adadin da suka yi niyyar saya saboda tashin farashi.

Dan kasuwan ya ce akwai yiwuwar samu karin sauki idan rage farashin mai da Matatar Dangote ta sanar ya yi tasiri a harkar sufuri, ta yadda za a samu sauki kudin jigilar amfanin gona daga kauyuka zuwa kasuwanni, kuma zai taimaka wa wajen rage kudin da manoman rani ke kashewa kan man fetur a injunansu na ban-ruwa.

Shinkafar waje ta fi ta gida sauki

Da ya ke bayani kan farashin kayan abincin, Alhaji Almustafa Imam ya ce, lamarin har ya kai ga shinkafa da kamfanonin gida ke sarrafawa tana neman fin wadda ake sayowa daga kasar waje saukin farashi.

“Idan zan yi misali da shinkafa da ake kawowa daga kasar Indiya, akwai wadda ake sayarwa a kan Naira dubu 87, a yayin da ta kamfanin gida kwatankwacinta mai nayin kilo 50 mai suna Big Bull ke kai naira dubu 89.” in ji dan kasuwan.

“A bangaren gero kuwa, na sayi buhu mai nauyi kilo 100 a kan naira dubu 72 a lokacin kaka, sai ga shi a yanzu ya karye ya koma naira dubu 62. Wake mafi daraja da ake kira ‘iron beans’ kuwa, na sayi buhu a kan naira dubu 130 a lokacin kaka, amma yanzu ya koma naira dubu dari da goma.

“Wake da ke biye da ‘iron beans’ a daraja a kan naira dubu 95 aka sayar da shi a lokacin kaka, sai ga shi a yanzu ana samun sa a kan naira dubu 80 a wuraren da ake zuwa sari kamar garin Kontagora, da ke jihar Neja, in ji dan kasuwan, wanda ya ce akwai nau’ukan wake da ba su kai wadannan daraja ba da ake samu a kan naira dubu 70.

Ya ce yakan sayi kayan ne a lokacin kaka ya ajiye don gudun bacin rana, amma sai ga shi wannan karon farashin ya karye.

Dan kasuwar ya bukaci gwamnati da ta wadata manoma da kayan aiki a damina mai zuwa don rage farashin abin da ake nomawa a cikin gida, maimakon dogaro da na waje, wanda ya ce ba shi da tabbas.

Kayan kamfani ma sun yi sauki 

Alhaji Muhammadu Dan Saleh da ke gudanar a kasuwanci a Babbar Kasuwar IBB da ke garin Suleja a Jihar Neja ya ce an samu saukin farashin kayan masarufi na kamfani kamar garin samambita da semolina da taliya da makaroni da sauransu.

Ya bayyana cewa kafin watan azumi suna sayar da kwalin taliya Mai Kwabo a kan naira dubu 17, amma yanzu ya karye ya koma kimanin naira dubu 15.

Taliyar Glden Penny kuma, a baya suna sayar da ita a kan naira dubu 21, amma a yanzu ta koma dubu 20.

Buhun sukari na Dangote mai nauyi kilo 50 da a baya ake sayarwa naira dubu 82, a ya koma naira dubu 79 duk da kamawar watan azumi.

Ya ce, wasu kayan na kara farashi ne a lokacin da aka fuskanci yankewarsu a kasuwa, inda ya bayar da misali da cewa “kwalin madarar ruwa ta Peak da a baya an yi lokacin da ta kai naira dubu 45, yanzu tana samuwa a kan naira dubu 43 duk da karuwar bukatarta da ake yi a lokaci irin wannan na watan azumi.”

Ga koshi ga kwanan yunwa

Wasu da Aminiya ta zanta da su sun yaba da saukin farashin kayan abincin da aka samu, sai dai sun yi korafin cewa idan ba a yi dace ba, ’yan kasuwan ne za su sake saye kayan, a nema a rasa a kasuwa.

Wani ma’aikacin gwamnati a yankin Babban Birnin Tarayya, Abuja, Malam Abdullahi Alamuna, ya ce ma’aikata da dama da ya kamata su ci gajiyar saukar farashin, ba a biya su albashinsu na watan Fabrairun da ya gabata ba, sai bayan kamawar sabon wata da kwana hudu.

Hakan, in ji shi, ya sa yawancinsu “ba su iya yin cefanen kayan abinci azumi ba a farkon watan, sannan kasuwanni ba su samu hadahada bayan karban albashi ba, sun kasance cikin karancin ciniki, duk kuwa da saukin kayan abincin da ka samu.”

Shi ma wani mazaunin Abuja, Malam Isa Adamu Rimin Kebe, ya ce “’yan kasuwa da dama a kasuwannin birni na kin sauke farashin kayan abinci duk da saukin da aka samu, inda suke la’akari da farashin tsohon kaya da suka sayo.”

Ya ci gaba da ceaw, “hakan ta sa jama’a da dama da ke neman cin gajiyar saukin da aka samu zuwa kasuwannin kauyuka don samun rangwamen da ya dace.

Hakan ya saba da lokacin da ake samun tashin farashin kayan abinci a kai-akai a baya, inda a wani lokaci waya kadai ’yan kasuwan ke yi da inda suke saro kaya, sai nan take su kara farashi.

Azumin bana sai godiya — Magidanta

Wani magidanci a garin Kaduna, Malam Umar Ramalan Direba, ya ce, “Gaskiya babu abin cewa sai godiya ga Allah, saboda azumin bana dai kam sai godiya ga Allah.

“Ko ba ka da kudin saye za ka ji dadin cewa abinci ya sauka. A bara gero mun saya dubu 1,400 mudu zuwa 1,500 amma sai ga shi a bana kasa da dubu daya.

 “’Yan kasuwa sun wasa wukarsu domin sayar wa jama’a kaya da tsada, amma sai ga shi Allah Ya kamasu, abubuwa suka yi sauki.

“Shi ya sa duk wani magidanci ya samu natsuwa ko da kuwa ba shi da kudin saya domin a bara babu kudi kuma kaya da tsada, ina amfani,” in ji shi.

Abdulmomin Babangida Shehu wani magidanci mai aikin gadi a Kaduna ya ce a yanzu an samu karin masu bayar da taimakon kayan abinci saboda abubuwa sun yi sauki.

“Duk da cewa ba muna son a bamu ba ne kyauta, amma idan abinci ya yi sauki kowa zai samu na ci da budabaki. Shi ya sa muke cikin jin dadi a bana. Domin akwai bayin Allah masu taimako don Allah, ke nan a bana za su samu damar kara taimakawa marasa galihu,” in ji shi.

Shi ma Rimi, wani mai sayar da man fetur a Mogadishi Kaduna cewa ya yi hakika magidanta “Muna cikin farin ciki a bana saboda saukin farashin kayan abinci da aka samu.

“Domin ba a taba samun saukin kayan abinci a lokacin Ramadan ba sai a bana. Sai dai akwai rashin kudi a hannun mutane amma duk da haka muna jin dadin, saukin da aka samu musamman a kasuwanni. Masu shaguna ne kurum suka ki yin sauki,” in ji shi.

Rimi ya kara da cewa a yanzu  masu cirani sun fi son su hada kudi su sayi kayan abinci su girka da kansu a kakunansu a maimakon su saya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: kasuwa Ramadan farashin kayan abincin farashin kayan abinci a kan naira dubu kayan abinci a saukin farashi watan azumi

এছাড়াও পড়ুন:

Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza

Kamfanin dillancin labarun “Reutres” ya bayyana cewa; Cibiyar da take tafiyar da ayyukan agaji a Gaza, wacce Amurka ta kafa ta, ta bayar da wata shawarar da take cewa; a kafa wa mutanen Gaza hemomi na wucin gadi da za su zama masomin yin hijirarsu zuwa wani wuri daban, a cikin yankin ko a wejensa.

Rahoton kamfanin dillancin labarun na Reuters ya ambato wata majiya mai karfi tana cewa; An gabatarwa da shugaban kasar Amurka shawarar tilastawa mutanen Gaza yin hijira, kuma a cikin kwanakin nan an tatauna wannan batu a fadar mulkin Amurka ta “White House.”

Har ila yau rahoton ya kunshi cewa,tun daga watan Febrairu cibiyar ta fara kokarin tara kudaden da za su kai dalar Amurka biliyan 1 domin aiwatar da Shirin hijirar mutanen Gaza a cikin yankin ko kuma zuwa wajensa, da kuma kwace makaman da suke a hannun ‘yan gwagwarmaya.

A karkashin wannan Shirin da akwai matakai guda uku; Na farko shi ne bayar da kayan agaji. Na biyu shi ne gina hemomi na tsugunar da Falasdinawa a cikinsu. Na uku shi ne fitar da mutanen Gaza zuwa hijira ta dole, wacce babu dadowa.

 A fili yake cewa a cikin matakin farko da har yanzu ake cikinsa, wurin da aka kira na raba kayan agaji, ba komai ba ne,sai tarko na kashe Faladinawa. Duk wanda ya je domin ya karbi kayan agaji, to ya zama abin farautar ‘yan sahayoniya.

Masu kula da wadannan cibiyoyin na agaji da aka kafa kuwa su ne; HKI da wata rundunar sojojin ‘yan ina da yaki ta Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Abinci Ta Duniya ( WFP) Ta Jefa Wa Mutanane Kudancin Sudan Abinci Ta Sama
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamaya Biyar Tare Da Jikkata Wasu Goma Na Daban
  • ASUU Ta Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Biya Albashin Watan Yuni
  • ASUU Ta Tsunduma Yajin Aiki A Faɗin Nijeriya
  • NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19
  • Reuters: Amurka Tana Da Shirin Korar Falasdinawa Daga Gaza
  • Hukumar Kula da Muhalli ta Jihar Jigawa ta Kwace Gurbatattun Kayayyaki na Miliyoyin Naira
  • Falasdinawa Kimani 635 Amurka da HKI Suka Kashe A Cibiyoyin Karban Abinci A Gaza
  • Tinubu ya umarci sojoji su murƙushe ’yan ta’adda a faɗin Najeriya 
  • Gobe Za A Fara Wasannin Kofin Afirka Na Mata