Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya
Published: 15th, March 2025 GMT
Ya ce fim ɗin tarihin zai nuna nasarori, ƙalubale, da darussan da aka koya a wannan tafiya.
Ya ce: “Na yi farin cikin ganin ƙoƙarin da IPAC da shugabannin ta suke yi wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya, musamman ta hanyar fim ɗin wanda zai zama wata muhimmiyar shaida ta tarihi, domin girmama jaruman siyasar ƙasar mu da kuma nuna jajircewar Nijeriya a harkar dimokiraɗiyya.
Ya jinjina wa IPAC kan jajircewar ta wajen cigaban dimokiraɗiyya tare da jaddada muhimmancin haɗin kan jam’iyyun siyasa bayan zaɓe domin ƙarfafa haɗin kan ƙasa da cigaba.
“Gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana goyon bayan a yi gasa mai kyau a siyasa, domin dimokiraɗiyya tana bunƙasa ne idan ana samun hamayya mai ma’ana da haɗin kai bisa muradin ƙasa ba tare da la’akari da bambancin jam’iyyun siyasa ba,” inji Idris.
Ya ƙara da cewa ɗorewar tsarin dimokiraɗiyya tana buƙatar haɗin gwiwa daga kowane ɓangare.
Ya ce: “Jam’iyyun siyasa su ne ginshiƙin dimokiraɗiyya; kuma yayin da hamayya take da muhimmanci a lokacin zaɓe, dole ne mu haɗa kai bayan haka don gina ƙasar mu.
“Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, wanda babban ɗan dimokiraɗiyya ne, yana mutunta gasa mai tsafta, amma yana kuma fifita haɗin kai da cigaban ƙasa.”
Shugaban IPAC na ƙasa, Honourable Yusuf Ɗantalle, ya ce shirin fim ɗin tarihin zai bayyana cigaban da aka samu a fannonin gina ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, da haɗin kan al’umma.
Ɗantalle ya ce: “Fim ɗin, a matsayin wani muhimmin tarihin ƙasa, zai mayar da hankali kan matasa, musamman ‘yan zamani (Gen Z), domin ya zama wata hanyar ilmantarwa da haɗe kan ‘yan ƙasa kan tafiyar dimokiraɗiyyar Nijeriya. Fim ɗin zai ƙunshi fitattun jaruman Nollywood kuma za a shirya shi da na’urori na zamani domin ya dace da matakin inganci na duniya.”
Daga cikin shugabannin IPAC da suka halarci taron akwai Mataimakin Ciyaman ɗin IPAC na Ƙasa Dipo Olayokun, da memba a majalisar, Cif Dan Nwayanwu, da Sakatare na Ƙasa, Maxwell Mabudem.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.
Ministan Noma Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta Jihar Jigawa.
Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.
Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.
Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.
A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.
Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.
Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.
Usman Muhammad Zaria