Ya ce fim ɗin tarihin zai nuna nasarori, ƙalubale, da darussan da aka koya a wannan tafiya.

 

Ya ce: “Na yi farin cikin ganin ƙoƙarin da IPAC da shugabannin ta suke yi wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya, musamman ta hanyar fim ɗin wanda zai zama wata muhimmiyar shaida ta tarihi, domin girmama jaruman siyasar ƙasar mu da kuma nuna jajircewar Nijeriya a harkar dimokiraɗiyya.

A kan haka, Gwamnatin Tarayya, ta hannun Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, za ta goyi bayan shirya wannan fim na musamman.”

 

Ya jinjina wa IPAC kan jajircewar ta wajen cigaban dimokiraɗiyya tare da jaddada muhimmancin haɗin kan jam’iyyun siyasa bayan zaɓe domin ƙarfafa haɗin kan ƙasa da cigaba.

 

“Gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana goyon bayan a yi gasa mai kyau a siyasa, domin dimokiraɗiyya tana bunƙasa ne idan ana samun hamayya mai ma’ana da haɗin kai bisa muradin ƙasa ba tare da la’akari da bambancin jam’iyyun siyasa ba,” inji Idris.

 

Ya ƙara da cewa ɗorewar tsarin dimokiraɗiyya tana buƙatar haɗin gwiwa daga kowane ɓangare.

 

Ya ce: “Jam’iyyun siyasa su ne ginshiƙin dimokiraɗiyya; kuma yayin da hamayya take da muhimmanci a lokacin zaɓe, dole ne mu haɗa kai bayan haka don gina ƙasar mu.

 

“Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, wanda babban ɗan dimokiraɗiyya ne, yana mutunta gasa mai tsafta, amma yana kuma fifita haɗin kai da cigaban ƙasa.”

 

Shugaban IPAC na ƙasa, Honourable Yusuf Ɗantalle, ya ce shirin fim ɗin tarihin zai bayyana cigaban da aka samu a fannonin gina ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, da haɗin kan al’umma.

Ɗantalle ya ce: “Fim ɗin, a matsayin wani muhimmin tarihin ƙasa, zai mayar da hankali kan matasa, musamman ‘yan zamani (Gen Z), domin ya zama wata hanyar ilmantarwa da haɗe kan ‘yan ƙasa kan tafiyar dimokiraɗiyyar Nijeriya. Fim ɗin zai ƙunshi fitattun jaruman Nollywood kuma za a shirya shi da na’urori na zamani domin ya dace da matakin inganci na duniya.”

 

Daga cikin shugabannin IPAC da suka halarci taron akwai Mataimakin Ciyaman ɗin IPAC na Ƙasa Dipo Olayokun, da memba a majalisar, Cif Dan Nwayanwu, da Sakatare na Ƙasa, Maxwell Mabudem.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC

Hukumar ICPC ta ce da ana aiwatar da dokokin yaƙi da cin hanci da rashawa yadda ya kamata, da kusan kashi 80 na ’yan Najeriya na ɗaure a gidan yari.

Kwamishinan ICPC na Jihar Kaduna, Sakaba Ishaku ne, ya bayyana haka a wani taron horaswa kan yadda ake kula da amana a ƙananan hukumomi.

Kisan Zariya: Na bar Buhari da Allah — Sheikh El-Zakzaky Najeriya za ta buga wasan sada zumunta da Masar kafin fara gasar AFCON ta 2025

Ya ce cin hanci ya yi tasiri sosai a rayuwar ’yan Najeriya, kuma yana haifar da talauci, rikice-rikice, da jinkirta ci gaban ƙasa.

Ya ƙara da cewa yawancin dukiyar da wasu ke taƙama da ita a Najeriya ma da alaƙa da aikata rashin gaskiya, kuma mutane da yawa ba sa son jin batun yaƙi da cin hanci saboda suna jin daɗin aikata shi.

Ishaku, ya soki shugabannin ƙananan hukumomi da ke barin kujerarsu ba tare da sun aiwatar da wani gagarumin aiki ba.

Ya kuma nemi a tsaurara hukunci ga masu satar dukiyar gwamnati, inda ya ce duk wanda ya saci dukiyar jama’a bai kamata a masa hukunci mai sauƙi ba.

Kwamishinan Harkokin Ƙananan Hukumomi na Kaduna, Sadiq Mamman Legas, ya goyi bayan bayanan ICPC.

Ya ce gwamnati ta gyara na’urorin wutar lantarki a wasu yankuna, amma mazauna wajen suka lalata, tare da suka sace wasu.

Ya ce ba za a samu ci gaba ba idan mutane suna lalata dukiyar gwamnati.

Dukkanin jami’an sun yi kira da a ƙara ƙarfafa doka, a kula da ayyukan gwamnati sosai, kuma a wayar da kan jama’a domin rage cin hanci da kare kayayyakin gwamnati.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • Gwamnatin Kano Ta Haramta Sabuwar Hisbah Da Ganduje Ke Shirin Ƙirƙirowa
  • 2027: Jam’iyyar NNPP ta rantsar da sabbin shugabanni a Gombe
  • Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya
  • Matatar man Dangote ta rage farashin fetur zuwa N699
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • NLC Ta Shirya Zanga-Zangar Rashin Tsaro A Faɗin Ƙasa Ranar 17 Ga Disamba
  • ‘Yan Siyasa Ne Ke Zagon Ƙasa Ga Ci Gaban Nijeriya — Sarki Sanusi II
  • Ba ni da shirin ficewa daga PDP — Gwamnan Bauchi
  • Cin hanci da rashawa sun yi ƙatutu a Najeriya — ICPC