Gwamnati Za Ta Goyi Bayan Shirin Fim Kan Tarihin Shekaru 25 Na Dimokuraɗiyyar Nijeriya
Published: 15th, March 2025 GMT
Ya ce fim ɗin tarihin zai nuna nasarori, ƙalubale, da darussan da aka koya a wannan tafiya.
Ya ce: “Na yi farin cikin ganin ƙoƙarin da IPAC da shugabannin ta suke yi wajen ƙarfafa dimokiraɗiyya, musamman ta hanyar fim ɗin wanda zai zama wata muhimmiyar shaida ta tarihi, domin girmama jaruman siyasar ƙasar mu da kuma nuna jajircewar Nijeriya a harkar dimokiraɗiyya.
Ya jinjina wa IPAC kan jajircewar ta wajen cigaban dimokiraɗiyya tare da jaddada muhimmancin haɗin kan jam’iyyun siyasa bayan zaɓe domin ƙarfafa haɗin kan ƙasa da cigaba.
“Gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu tana goyon bayan a yi gasa mai kyau a siyasa, domin dimokiraɗiyya tana bunƙasa ne idan ana samun hamayya mai ma’ana da haɗin kai bisa muradin ƙasa ba tare da la’akari da bambancin jam’iyyun siyasa ba,” inji Idris.
Ya ƙara da cewa ɗorewar tsarin dimokiraɗiyya tana buƙatar haɗin gwiwa daga kowane ɓangare.
Ya ce: “Jam’iyyun siyasa su ne ginshiƙin dimokiraɗiyya; kuma yayin da hamayya take da muhimmanci a lokacin zaɓe, dole ne mu haɗa kai bayan haka don gina ƙasar mu.
“Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, wanda babban ɗan dimokiraɗiyya ne, yana mutunta gasa mai tsafta, amma yana kuma fifita haɗin kai da cigaban ƙasa.”
Shugaban IPAC na ƙasa, Honourable Yusuf Ɗantalle, ya ce shirin fim ɗin tarihin zai bayyana cigaban da aka samu a fannonin gina ababen more rayuwa, kiwon lafiya, ilimi, da haɗin kan al’umma.
Ɗantalle ya ce: “Fim ɗin, a matsayin wani muhimmin tarihin ƙasa, zai mayar da hankali kan matasa, musamman ‘yan zamani (Gen Z), domin ya zama wata hanyar ilmantarwa da haɗe kan ‘yan ƙasa kan tafiyar dimokiraɗiyyar Nijeriya. Fim ɗin zai ƙunshi fitattun jaruman Nollywood kuma za a shirya shi da na’urori na zamani domin ya dace da matakin inganci na duniya.”
Daga cikin shugabannin IPAC da suka halarci taron akwai Mataimakin Ciyaman ɗin IPAC na Ƙasa Dipo Olayokun, da memba a majalisar, Cif Dan Nwayanwu, da Sakatare na Ƙasa, Maxwell Mabudem.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Dalilin yawaitar juyin mulki a Afirka ta Yamma
Masana harkokin siyasa, jakadu da ƙungiyoyin fararen hula sun bayyana cewa rashin shugabanci nagari da son mulki na dogon lokaci su ne manyan dalilan da ke haddasa yawaitar juyin mulki a yankin Afirka ta Yamma.
Wannan na zuwa ne bayan yunƙurin juyin mulki da aka yi a Jamhuriyar Benin a ranar Lahadi, wanda ya jefa ƙasar cikin rudani.
Gwamnatin Benin ta ce ta shawo kan lamarin bayan wasu sojoji sun bayyana a talabijin na ƙasar cewa sun kifar da Shugaba Patrice Talon. Wannan na zuwa ne makonni kaɗan bayan juyin mulki a ƙasar Guinea-Bissau.
Majiyoyin tsaro sun tabbatar da kama sojoji kusan 12, ciki har da shugabannin yunƙurin da bai yi nasara ba. Talon, tsohon ɗan kasuwa mai shekaru 67, na shirin miƙa mulki a watan Afrilu mai zuwa bayan shekaru 10 a kan karagar mulki da ake ganin ya kawo ci gaban tattalin arziki da kuma ƙaruwar hare-haren masu iƙirarin jihadi.
Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman NajeriyaSojojin da suka kira kansu Kwamitin Soja na Sake Tsarawa (CMR) sun bayyana a talabijin cewa sun yanke hukuncin cire Talon daga mulki.
Sai dai daga baya fadar shugaban ƙasa ta tabbatar da cewa Talon yana cikin koshin lafiya, ya ƙ bayyana masu yunƙurin a matsayin “ƙananan mutane da suka mamaye talabijin kawai.”
Ra’ayin masanaJakadan Najeriya a ƙasashen yankin, Ambasada Suleiman Ɗahiru, ya ce juyin mulki na yawaita ne saboda raunin dimokuradiyya da kuma rashin nagartar shugabanci.
“Dimokuradiyya ba ta kafa tushe yadda ya kamata a Afirka ta Yamma. Shugabanni da aka zaɓa ba sa tafiyar da ƙasashensu yadda ya dace, hakan ya haifar da ƙin yarda daga jama’a,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa zaɓe ya rasa amincewa a ƙasashe da dama, inda shugabanni ke ƙin sauka daga mulki. Ya kawo misali da Kamaru, inda shugaban ƙasa mai shekaru 92 ya ci zaɓe, da Gambiya, inda shugabanni ke nuna rashin niyyar sauka daga mulki.
Suleiman Ɗahiru ya ce sai shugabanni sun yi mulki da gaskiya da adalci, in ba haka ba, juyin mulki zai ci gaba da dawowa.
Ƙalubalen ECOWASTsohon jakadan Najeriya, M.K Ibrahim, ya bayyana cewa yawaitar juyin mulki babban koma baya ne ga yankin da kuma ƙungiyar ECOWAS.
Ya ce tun bayan kafa ECOWAS a 1975, an samu aƙalla juyin mulki 45 a yankin, sai dai tsakanin 2000 zuwa 2008 ne kawai aka samu zaman lafiya ba tare da juyin mulki ba.
Ibrahim ya ce yunƙurin da bai yi nasara ba a Benin ya sake bayyana raunin dimokuradiyya a yankin. Yanzu ƙasashe huɗu na ECOWAS ke ƙarƙashin mulkin soja, kuma idan Benin ta faɗi, da za a ce sun zama biyar.
Ya ce Najeriya na da nauyi na musamman wajen tabbatar da ci gaba da rayuwar ECOWAS, duk da matsalolinta na siyasa da tattalin arziki.
Ra’ayoyi kan matakan ECOWASIbrahim ya bayyana cewa akwai ra’ayoyi biyu a cikin ƙungiyar:
– Wasu na ganin dole a tsaya kan ka’idojin dimokuraɗiyyar da nagartar shugabanci, ko da hakan zai sa ƙasashe su fice daga ECOWAS.
– Wasu kuma na ganin ka’idojin sun yi tsauri, suna ba da shawarar tattaunawa maimakon fitar da ƙasa nan take.
Sai dai Ibrahim ya bayyana matsayinsa: “ECOWAS ba za ta ci gaba ba ta hanyar juyin mulki. Dimokuraɗiyya da nagartar shugabanci ne kawai za su tabbatar da haɗin kai da ci gaba.”
Dalilan yawaitar juyin mulkiYa ce raunin dimokuraɗiyyar, talauci, rashin tsaro da matsalolin Sahel na daga cikin manyan dalilan da ke sa jama’a su rungumi alkawarin sojoji duk da rashin tabbas.“Ba za a iya cewa akwai wata ƙasa a Afirka da ta tsallake barazanar juyin mulki ba,” in ji shi.
Daga: Sagir Kano Saleh, Joshua Odeyemi, Baba Martins, Dalhatu Liman (Abuja) & Salim Umar Ibrahim (Kano)