Minista ya caccaki El-Rufai kan sukar Tinubu da APC
Published: 15th, March 2025 GMT
Ƙaramin Ministan Gidaje da Raya Birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya caccaki Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan sukar jam’iyyar APC da kuma Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
A cikin wata sanarwa da hadiminsa, Seyi Olorunsola, ya fitar, ministan ya zargi El-Rufai da haddasa rikici saboda bai samu muƙamin minista ba.
Ya ce tsohon gwamnan mutum ne da ƙware wajen haddasa ce-ce-ku-ce da kuma yanke tsauraran hukunci a harkokin siyasa.
Ata ya ce lokacin da El-Rufai yake gwamnan Kaduna, an samu matsaloli da suka haɗa da rashin tsaro, rikicin ƙabilanci da addini.
Ya kuma ce komawar El-Rufai jam’iyyar SDP wata hanya ce da yake ƙoƙarin amfani da ita don a ci gaba da dama da shi a fagen siyasa.
Ministan ya yi watsi da iƙirarin El-Rufai na cewa Tinubu yana haddasa rikici a jam’iyyun adawa, inda ya ce wannan magana ba ta da tushe.
Ya jinjina wa Tinubu bisa jajircewarsa da ƙwarewarsa wajen bunƙasa siyasa, saɓanin El-Rufai da ya ce mutum ne da ke canza jam’iyya akai-akai don son zuciya.
Ata, ya tabbatarwa da ’yan Najeriya cewa APC na ƙoƙarin ci gaba da gina ƙasa, inda ya buƙace su da kada su saurari kalaman El-Rufai.
Ya ce gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da aiki tuƙuru wajen bunƙasa tattalin arziƙi, bunƙasa ababen more rayuwa da tabbatar da tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Arakci Ya Jaddada Muhimmanci Kawo Karshen Yakin Gaza Da Kuma Shigar Da Kayan Agaji
Ministan harkokin wajen Jamhuriyar Musulunci ta Iran, Abbas Arakci wanda ya gana da takwransa na fadar Vatican ya yi kira da a kawo karshen laifukan da ‘yan mamaya suke tafkawa akan Gaza da gaggawa a kuma shigar da kayan agaji zuwa yankin.
Ministan harkokin wajen na Iran wanda ya je kasar Italiya domin tattaunawar bayan fage da Amurka akan Shirin kasarsa na Nukiliya, ya ziyarci fadar Vatican, inda ya gana da ministanta na harkokin wajen Cardinal paul Gallagher, ya mika sakon ta’aziyyar rasuwar Fafaroma Farancis sannan kuma da murnar zabar sabon Fafaroma Leo na 14
Abbas Arakci ya yi wa shugabannin fadar ta Vatican bayani akan matsayar Jamhuriyar musulunci ta Iran dangane da shirinta na Nukiliya na zaman lafiya, da kuma inda aka kwana a tattaunawar bayan fage da Amurka.
Haka nan kuma ya yi bayani akan matsayar Iran akan kisan kiyashin da ake yi wa al’ummar Gaza, tare da yin kira da a kawo karshensa da kuma shigar da kayan agaji zuwa yankin.
Haka nan kuma ya yi bayani akan yadda Iran take ganin za a iya warware matsalar mamaya a Falasdinu da ita ce yin kuri’ar raba gardaga da dukkanin Falasdinawa,musulmi kiristoci da yahudawa za su shiga a ckin tsarin demokradiyya.
A karshe bangarorin biyu sun jaddada muhimmanci tattaunawa a tsakanin addinai domin shimfida sulhu da zaman lafiya.