Minista ya caccaki El-Rufai kan sukar Tinubu da APC
Published: 15th, March 2025 GMT
Ƙaramin Ministan Gidaje da Raya Birane, Yusuf Abdullahi Ata, ya caccaki Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, kan sukar jam’iyyar APC da kuma Gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
A cikin wata sanarwa da hadiminsa, Seyi Olorunsola, ya fitar, ministan ya zargi El-Rufai da haddasa rikici saboda bai samu muƙamin minista ba.
Ya ce tsohon gwamnan mutum ne da ƙware wajen haddasa ce-ce-ku-ce da kuma yanke tsauraran hukunci a harkokin siyasa.
Ata ya ce lokacin da El-Rufai yake gwamnan Kaduna, an samu matsaloli da suka haɗa da rashin tsaro, rikicin ƙabilanci da addini.
Ya kuma ce komawar El-Rufai jam’iyyar SDP wata hanya ce da yake ƙoƙarin amfani da ita don a ci gaba da dama da shi a fagen siyasa.
Ministan ya yi watsi da iƙirarin El-Rufai na cewa Tinubu yana haddasa rikici a jam’iyyun adawa, inda ya ce wannan magana ba ta da tushe.
Ya jinjina wa Tinubu bisa jajircewarsa da ƙwarewarsa wajen bunƙasa siyasa, saɓanin El-Rufai da ya ce mutum ne da ke canza jam’iyya akai-akai don son zuciya.
Ata, ya tabbatarwa da ’yan Najeriya cewa APC na ƙoƙarin ci gaba da gina ƙasa, inda ya buƙace su da kada su saurari kalaman El-Rufai.
Ya ce gwamnatin Tinubu za ta ci gaba da aiki tuƙuru wajen bunƙasa tattalin arziƙi, bunƙasa ababen more rayuwa da tabbatar da tsaro.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Ta kuma ba shi umarnin ya goge rubutun da ta ce ya ci zarafin shugaban ƙasa.
Sai dai Sowore ya ƙi sauke rubutun da ya wallafa.
Ya rubuta a shafinsa na X cewa: “DSS ta shigar da ƙara mai tuhuma biyar a Babbar Kotun Tarayya a Abuja a kaina, X da kuma Facebook.
“Sun ce wai na aikata wasu sabbin laifuka saboda na kira Tinubu ‘ɓarawo’. Duk da haka, zan halarci kotu duk lokacin da aka fara shari’ar.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp