Aminiya:
2025-07-04@18:09:36 GMT

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno

Published: 4th, July 2025 GMT

Dakarun Rundunar ‘Operation Haɗin Kai’ sun kashe ’yan ta’adda biyu tare da ƙwato makamai da kayan aiki a wani ƙazamin artabu da suka yi a hanyar Pulka zuwa Kirawa a Jihar Borno.

Majiyoyin soja sun bayyana cewa, a ranar Alhamis ne aka yi arangamar a yayin da sojoji suka yi artabu da wasu gungun ’yan ta’adda da ke yunƙurin tsallakawa zuwa yankin Dar-Jamal da ke kusa da Axis na Miyanti.

Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa ’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – Wike

Rikicin da ya yi sanadin ci gaba da musayar wuta, ya kai ga halaka ’yan ta’adda biyu, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Kayayyakin da aka ƙwato daga wurin sun haɗa da: bindigogi ƙirar AK-47 ɗauke da harsasai da Babura da rediyon Baofeng da wayoyin salula da magungunan kashe ƙwayoyin cuta da magunguna na ruwa da ƙananan na’urorin masu tara hasken rana, waɗanda ake kyautata zaton ’yan ta’addan na amfani da su wajen gudanar da ayyukansu.

Sojojin sun ci gaba da bibiyar ’yan ta’addan da suka tsere a wani mataki na ci gaba da kai hare-hare a yankin baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Operation Haɗin Kai Rundunar Sojoji yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya

Iran ta nuna makamai masu linzami wadanda suka bude kofofin jahannama kan ‘yan sahayoniyya

A martanin da gwamnatin yahudawan sahayoniyya suka kai wa Iran, sojojin Iran da dakarun kare juyin juya halin Musulunci na kasar sun nuna karfinsu na soji a matsayin wani bangare na “Alkawarin Gaskiya na 3”, inda suka harba daruruwan makamai masu linzami na ballistic da hypersonic.

A wani bangare na wannan harin na ramuwar gayya, Iran ta kai jerin hare-hare na hadin gwiwa, wanda kaso mafi tsoka na makamai masu linzami kamar Emad, Ghadr, Fattah 1, Sejjil da Khaybar.

A halin yanzu rahotonni da hotuna daga haramtacciyar kasar Isra’ila suna kara fitowa kan yadda makamai masu linzamin Iran suka tarwatsa wurare masu muhimmanci na gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ‘yan mamaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
  • Ayyukan ‘Yan Ta’adda Na Barazana Ga Shirin Gwamnati Na Wadata Kasa Da Abinci
  • Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • Lakurawa sun kashe mutum 15 a harin ramuwar gayya a Sakkwato
  • Amurka ta dakatar da bai wa Ukraine tallafin makamai
  • Kasar Iran Ta Nuna Ire-Iren Makamai Masu Linzami Da Ta Mayar Da Martani Da Su Kan ‘Yan Mamaya
  • An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin