Aminiya:
2025-09-18@00:18:14 GMT

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno

Published: 4th, July 2025 GMT

Dakarun Rundunar ‘Operation Haɗin Kai’ sun kashe ’yan ta’adda biyu tare da ƙwato makamai da kayan aiki a wani ƙazamin artabu da suka yi a hanyar Pulka zuwa Kirawa a Jihar Borno.

Majiyoyin soja sun bayyana cewa, a ranar Alhamis ne aka yi arangamar a yayin da sojoji suka yi artabu da wasu gungun ’yan ta’adda da ke yunƙurin tsallakawa zuwa yankin Dar-Jamal da ke kusa da Axis na Miyanti.

Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisa ’Ya’yana na da ’yancin mallakar filaye a Abuja – Wike

Rikicin da ya yi sanadin ci gaba da musayar wuta, ya kai ga halaka ’yan ta’adda biyu, yayin da wasu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Kayayyakin da aka ƙwato daga wurin sun haɗa da: bindigogi ƙirar AK-47 ɗauke da harsasai da Babura da rediyon Baofeng da wayoyin salula da magungunan kashe ƙwayoyin cuta da magunguna na ruwa da ƙananan na’urorin masu tara hasken rana, waɗanda ake kyautata zaton ’yan ta’addan na amfani da su wajen gudanar da ayyukansu.

Sojojin sun ci gaba da bibiyar ’yan ta’addan da suka tsere a wani mataki na ci gaba da kai hare-hare a yankin baki ɗaya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Operation Haɗin Kai Rundunar Sojoji yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta

Ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar Sin ya gudanar da taron manema labarai da misalin karfe 10 na safiyar yau Litinin, inda kakakin hukumar kididdiga ta kasar, kuma babban masanin tattalin arziki, kana daraktan sashen kididdigar tattalin arziki na kasar, Fu Linghui ya yi karin haske kan ayyukan tattalin arzikin kasar cikin watan Agustan bana, tare da amsa tambayoyin manema labarai.

A cewar bayanan da aka gabatar a yayin taron, ayyukan tattalin arzikin kasar a watan Agusta sun samu ci gaba ba tare da tangarda ba. Kuma hakan ya bayyana ne ta hanyoyi daban-daban kamar haka: masana’antu sun habaka cikin sauri, masana’antar kera kayayyakin aiki da masana’antar fasaha sun samu ci gaba mai kyau. Kana ayyukan bayar da hidima su ma sun bunkasa cikin sauri. Baya ga haka, an samu ci gaba mai kyau a bangaren bayar da hidimomi na zamani. Harkokin kasuwanci sun samu ci gaba cikin natsuwa, inda harkokin sayar da kayayyaki ga masu sayayya suka kara habaka. Har ila yau, kadarorin jari sun ci gaba da karuwa, jarin masana’antu ya habaka cikin sauri, harkokin fice da shigen kayayyaki sun ci gaba da girma, tsarin kasuwanci ya ci gaba da ingantuwa, kana yanayin samar da guraben aikin yi, ya kasance kan wani mataki mai daidaito. Sai dai kuma saboda yanayin da ake ciki, adadin marasa aikin yi a birane ya karu, ma’aunin Core CPI ya ci gaba da hauhawa, kana faduwar farashin kayayyakin masana’antu ya ragu.

Bayanan sun kara da cewa, akwai bukatar lura da cewa, ana fuskantar yanayin rashin tabbas a waje, kuma tattalin arzikin kasar Sin yana fuskantar kalubale da hadari da yawa. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa
  • Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno
  • Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba
  • Kungiyar Kare Hakkokin Bil’Adama Ta Siriya Ta Bankado Karin Fararen Hula Da Aka Kashe A Rikicin Suweida
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Espania Ta Soke Cinikin Makamai Na EUR Miliyon 700 Da HKI Saboda Kissan Kiyashi A Gaza
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000