Ambaliya da iska sun lalata gidaje 171 a Gombe — SEMA
Published: 4th, July 2025 GMT
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Gombe (SEMA), ta ce ambaliya da iska mai ƙarfi sun lalata gidaje 171 a wasu yankunan jihar cikin watanni biyu da suka wuce.
Wannan iftila’in ya jawo asara da kuma rasuwar yara huɗu.
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno Kotu ta umarci a mayar da Sanata Natasha majalisaSakataren hukumar, Malam Abdullahi Haruna Abdullahi ne, ya bayyana wa manema labarai a Gombe cewa ambaliya da iska sun shafi ƙananan hukumomin Dukku, Kwami, Gombe da Akko.
Ya ce: “An samu rushewar gidaje 87 a Dukku, 27 a Kwami, 30 a Gombe, da kuma 27 a Akko.
“Haka kuma wata coci ta lalace. Mafi yawan mutanen da suka mutu yara ne guda huɗu.”
Ya ce rashin tsaftar muhalli da sare bishiyoyi na taimakawa wajen haifar da irin wannan iftila’i.
Ya roƙi mutane da su guji zubar da shara a cikin magudanan ruwa, su kuma yi amfani da wuraren da gwamnati ta tanada domin zubar da shara.
“Dole ne kowa ya taimaka wajen kare muhalli, musamman a lokacin damina. Iyaye su kula da yara domin guje wa hatsari,” in ji shi.
Abdullahi ya kuma nuna damuwarsa kan yadda mutane ke sare bishiyoyi don yin gawayi da girki, inda ya bayyana cewa hakan yana kawo fari da lalacewar muhalli.
Ya shawarci mutane da su yi amfani da damina wajen dasa bishiyoyi a gidaje da unguwanni domin rage hatsarin iska da kuma hana ƙara yaɗuwar hamada.
Hakazalika, ya ce SEMA na shirin kai kayan agaji ga mutanen da ambaliya da iska suka shafa a sassan jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ambaliya
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
Aƙalla masallata 40 ’yan bindiga suka sace a wani masallaci da ke Gidan Turbe a Karamar Hukumar Tsafe ta Jihar Zamfara da safiyar wannan Litinin.
Majiyoyi sun ce an yi awon gaba da masallatan ne zuwa dazukan Gohori da ke yankin Tsafe.
Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a LegasWannan harin dai kai tsaye masu ruwa da tsaki na kallonsa a matsayin kawo ƙarshen yarjejeniyar sulhu tsakanin ’yan bindigar da mahukuntan jihohin Zamfara da Katsina.
A baya-bayan nan ne jihohin Katsina da Zamfara suka ƙulla yarjejeniyar sulhu tsakaninsu da ’yan bindigar da suka addabi al’ummar jihohin arewa maso yammacin Najeriyar.
Yarjejeniyar sulhu da aka cimma a dajin Wurma ta samu halartan manyan ’yan bindiga irinsu Alhaji Usman Kachalla Ruga da Muhindinge da Yahaya Sani ( Hayyu ) da kuma Shu’aibu.
A ɓangaren mahukunta, akwai Maradin Katsina da Hakimin Kurfi, Alhaji Mansur Amadu Kurfi da kuma shugaban ƙaramar hukuma Babangida Abdullahi Kurfi.
’Yan bindiga sun saki wasu mutane da suke garkuwa da su a lokacin yarjejeniyar sulhun, tare da barin al’umma zuwa gonakinsu ba tare da wata fargaba ko tsangwama.
To sai dai kuma, ƙasa da wata guda bayan cimma wannan yarjejeniya, rahotanni sun ce ’yan bindiga sun kutsawa wani ƙauye a Zamfara tare da awon gaba da masallata.
Shaidun gani da ido sun ce, maharan sun yi wa masallacin ƙawanya da misalin ƙarfe 5:30 na safe, daidai lokacin da jama’a ke sallar asuba.