Aminiya:
2025-06-16@02:24:36 GMT

’Yan bindiga na neman N30m domin fansar gwarzon gasar Al-Qur’ani a Katsina

Published: 15th, March 2025 GMT

’Yan bindigar da suka yi garkuwa da wani gwarzon musabaƙar karatun Al-Qur’ani a Jihar Katsina, Abdulsalam Rabi’u Faskari, suna neman naira miliyan 30 a matsayin kuɗin fansa

Da yake zantawa da manema labarai a ranar Juma’a, Kwamishinan watsa labarai da al’adu na Katsina, Bala Salisu-Zango ya ce Abdulsalam da mahaifinsa da ɗan uwansa da ’yan bindiga suka yi garkuwa da su, suna nan da ransu a hannun ’yan bindiga, ba a kashe su ba.

’Yan Nijeriya su ƙara haƙuri kan matakan da muke ɗauka — Tinubu Minista ya caccaki El-Rufai kan sukar Tinubu da APC

Ya ce “Gwamnati ta samu labarin wani saƙon jaje da ake yaɗawa wanda mai ba gwamnan jihar Kebbi shawara kan harkokin watsa labarai ya sa wa hannu, wanda ke nuna cewa ƴanbindiga sun kashe gwarzon musabakar karatun Al-Qur’ani na Najeriya, Abdussalam Rabiu-Faskari.

“Muna godiya da kulawar gwamnatin Kebbi, amma muna bayyana wa duniya cewa Rabiu-Faskari da mahaifinsa da ɗan uwansa suna nan da ransu cikin ƙoshin lafiya a hannun ’yan bindigar.”

Salisu-Zango ya ƙara da cewa ’yan bindigar suna neman kuɗin fansa har naira miliyan 30 ne domin sako mutanen.

Ya ce gwamnati za ta yi duk mai yiwuwa domin ceto su, tare da tabbatar da cewa sun koma gida lafiya, yana mai jaddada cewa gwamnatin jihar na ƙoƙari matuƙa domin magance matsalar rashin tsaro a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, a yammacin ranar Talatar da ta gabata ce ’yan bindigar suka sace mutanen a kusa da Labin Bangori, yayin da suke dawowa Faskari bayan Abdulsalam ya samu lambar yabo wadda Gwamna Dikko Radda ya ba shi saboda nasarar da ya samu a gasar karatun Alƙur’ani ta ƙasa karo na 39 da aka gudanar a Jihar Kebbi.

Abdulsalam, wanda ɗalibi ne a sashen likitanci na Jami’ar Ahmadu Bello (ABU), Zariya, shi ne ya zo na ɗaya a musabaƙar a ɓangaren maza.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Bindiga Abdulsalam Rabi u Faskari Jihar Katsina yan bindigar

এছাড়াও পড়ুন:

Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi

Bayan hakan, Pogba ya kunce kwantiraginsa da Juventus a watan Nuwamban 2024, kuma tun watan Maris da ya gabata ya samu damar komawa fili domin shirya dawowarsa.

Yanzu haka yana ci gaba da atisaye tare da fatan ƙulla sabuwar yarjejeniya da Monaco domin ci gaba da taka leda a ƙasarsa ta haihuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Sakkwato bai karɓi shanun tallafin layya ba — Hukumar Zakka
  • HOTUNA: Yadda aka yi sulhu da ƙasurgumin ɗan fashin daji Ado Aliero a Katsina
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • DA ƊUMI-ƊUMI: Gwamnati Ta Janye Taron Addu’ar Neman Wadatar Abinci
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
  • Gwamnatin Bauchi Ta Fara Shirin Kirkirar Sabbin Masarautu Da Sarakuna Da Gundumomi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina