Leadership News Hausa:
2025-10-16@00:13:58 GMT

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Published: 4th, July 2025 GMT

Kayayyakin Sin Na Kara Samun Karbuwa A Kasuwar Duniya

Kwanan baya, wasu kamfanonin samar da kayan shayi masu tamburan kasar Sin sun jawo hankalin sassan kasa da kasa, sakamakon yadda suka fara sayar da hannayen jarinsu a kasuwar hannayen jari ta kasa da kasa. Baya ga haka, wasu kayayyaki masu tamburan kasar Sin na kara samun karbuwa a kasuwannin duniya.

Har ma wasu kafofin yada labarai na kasa da kasa sun yi sharhin cewa, kayayyakin kasar Sin sun daina kwaikwayon wasu, suna bayyana halayensu na musamman a gaban jama’ar duniya.

Wadannan kayayyakin kasar Sin suna samun karbuwa a kasuwannin duniya ne sabo da fasahohin zamani da al’adu da ke tattare da su da ma yadda aka tsara fasalinsu, kuma hakan ya faru ne sakamakon cikakken tsarin samar da kayayyaki da yanayin kasuwa mai bude kofa da adalci a kasar, da ma yadda kasar ta dade tana dukufa a kan kirkire-kikire da kuma samun ci gaba mai inganci.

Shiga kasuwannin duniya da kayayyakin kasar Sin suka yi na bai wa masu sayayya na duniya damar samun karin zabi. A sa’i daya kuma, Sin na maraba da zuwan karin kamfanonin ketare masu ingantattun tamburan kasar, ta yadda za a yi koyi da juna da samun ci gaba tare, don al’ummun duniya su ci gajiyar dunkulewar tattalin arzikin duniya. (Mai zane da rubutu: MINA)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An Bukaci An Bukaci Asusun JICHIMA Ya Fadada Hanyoyin Samun Kudade Baya Ga Gwamnatin Jigawa

Kwamatin harkokin lafiya na majalisar dokokin jihar Jigawa ya ce gyaran fuskar da aka yiwa dokar da ta kafa asusun adashen gata na kiwon lafiya na jihar ya sahalewa asusun damar samo kudade daga wasu bangarori da ba na gwamnati ba.

Shugaban kwamatin kuma wakilin mazabar Guri, Alhaji Usman Abdullahi Tura Musari, ya yi wannan tsokaci lokacin da ya jagoranci ‘yan kwamatin domin ziyarar aiki a ofishin asusun da ke Dutse.

Ya bayyana bukatar ganin asusun JICHIMA ya nemo kudade daga hannun masu taimakon al’umma da cibiyoyi da ‘yan siyasa da kwamitocin zakka da na waqafi domin bunkasa asusun, ta yadda zai biya bukatun kiwon lafiyar al’ummar jihar.

Alhaji Usman Musari ya lura cewar fadada hanyoyin samun kudade ga asusun JICHIMA fiye da abinda ake yanka daga albashin ma’aikata zai tabbatar da ingancin aiki da kuma dorewar asusun.

Daga nan sai Alhaji Usman Musari ya shawarci asusun JICHIMA da ya rubanya kokari wajen kafa ofishinsa a dukkan kananan hukumomin jihar 27 domin biyan bukatun wadanda su ka yi rijista da asusun.

A nasa jawabin, wakilin mazabar Gwiwa Alhaji Aminu Zakari ya yi kira ga asusun JICHMA da ya inganta ayyukan sa a dukkan asibitocin da aka yiwa rijista domin gudanar da ayyukan asusun kamar yadda doka ta tanadar.

Da ya ke mayar da jawabi, Shugaban  Asusun Inshorarar Lafia na jihar Jigawan, Pharmacist Hamza Maigari Kakudi ya ce an kafa asusun ne da nufin kawar da nakasu wajen kiwon lafiyar jama’a ta hanyar tabbatar da cewar masu rauni a cikin al’umma sun samu kulawar da ta kamata.

Ya ce asusun yana shirin kaddamar da gangamin wayar da kan jama’a domin yin rijista ga masu karamin karfi 1000 a kowacce mazaba, domin cimma kudurin gwamnatin Malam Umar Namadi na kula da lafiyar jama’a.

A lokacin ziyaran, jami’an JICHIMA da kwamatin majalisar sun tattaunawa kan batun samar da ofis na dindindin ga asusun.

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Bukaci An Bukaci Asusun JICHIMA Ya Fadada Hanyoyin Samun Kudade Baya Ga Gwamnatin Jigawa
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Super Eagles Murnar Samun Cancantar Shiga Gasar Kwallon Kafa Ta Duniya
  • Yansandan Italiya Sun Kara Da Masu Goyon Bayan Falasdinawa A Garin Udine
  • Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima
  • Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
  • Shawarwarin Sin Sun Bude Sabuwar Hanyar Bunkasa Ci Gaban Mata A Duniya
  • An Janye Wajibcin Samun Kiredit A Darasin Lissafi Ga Ɗaliban Fannin Zamantakewa Don Shiga Manyan Makarantu 
  • Rasha ta kai wa tawagar kayan agajin MDD hari a Ukraine
  • Nazarin CGTN: Jama’ar Duniya Sun Jinjinawa Rawar Da Mata Ke Takawa A Harkokin Ci Gaba
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya