Aminiya:
2025-06-16@04:04:09 GMT

’Yan Nijeriya su ƙara haƙuri kan matakan da muke ɗauka — Tinubu

Published: 15th, March 2025 GMT

Shugaba Bola Tinubu ya buƙaci ’yan Nijeriya da su ƙara haƙuri kan matakan da gwamnatinsa ke ɗauka domin kawo ci gaba a ƙasar.

Tinubu ya ce duk da cewa gwamnatinsa mai sauraron koken jama’a ce, amma yana so a ƙara haƙuri domin akwai haske nan gaba.

Minista ya caccaki El-Rufai kan sukar Tinubu da APC Sojoji sun hallaka shugabannin ’yan bindiga 2 da wasu a Katsina 

Wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya fitar, ta ruwaito Tinubu yana wannan furuci ne a ranar Juma’a, yayin da ya karɓi baƙuncin ƙungiyar fastocin Cocin Katolika ta Catholic Bishop’s Conference of Nigeria (CBCN) a Fadar Shugaban Ƙasa da ke Abuja.

Ya bayyana wa malaman cocin cewa ya ɗauki matakai masu tsauri bayan ya karɓi mulki a shekarar 2023, ciki har da cire tallafin man fetur.

“Lallai cire tallafin man fetur mataki ne mai tsauri, amma ya zama dole ne domin ba za mu ci gaba da jinginar da ƙasarmu ba,” in ji shi.

“Sai dai akwai alamun nasara da sauƙi a gaba. Ana bayyana abubuwa masu kyau game da Nijeriya, kuma ina alfahari da haka. Matakan nan masu tsauri yanzu sun fara nuna alamomi masu kyau.”

Ya ce damina ta yi albarka wanda hakan ya sa farashin kayan abinci yake sauka, sannan farashin man fetur ma yana sauka.

A game da batun hare-haren ta’addanci, Tinubu ya ce rashin tsaro yana shafar musulmi da kirista, inda ya ƙara da cewa matarsa kirista ce, don haka ba zai zama mai yi musu kisan mummuƙe ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada

Kwamandan  sararin samaniya na dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Janar Amir Ali Haji Zadeh yana cikin wadanda su ka yi shahada sanadiyyar harin da sojojin HKI su ka kawo wa  da asubahin yau Juma’a.

Kamfanin dillancin labarun “Mehr” ya nakalto majiyar juyin juya halin musulunci ta Iran tana tabbatar da shahadar Janar  Amir Ali Haji Zadeh.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matatar Dangote Zata Fara Rarraba Man Fetur Da Dizal A Nijeriya
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • Nijeriya Ce Ta 3 A Manyan Kasashe Masu Karfin Masana’antu 10 Na Afirka
  • Yadda Badakalar Tallafin Man Fetur Ta Zame Wa Nijeriya Alakakai