Gwamnatin Jihar Neja ta bayyana cewa ya zama wajibi ta yi duk mai yiwuwa don tabbatar da yaki da rashin tsaro a kafatanin kananan hukumomi ashirin da biyar na jihar

 

Kwamishinan Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida na Jihar Neja, Birgediya Janar Mohammad Bello Abdullahi, ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi ga manema labarai a taron shirye-shiryen babban taron tsaro da za a gudanar a Minna.

 

Janar Mohammad Bello Abdullahi ya kara da cewa Gwamnati jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen yaki da rashin tsaro, inda ya bukaci hadin gwiwa daga kowane bangare domin cimma burin da aka sanya a gaba.

 

A cewarsa, babban taron zaman lafiya da tsaro na farko da za a gudanar a Jihar Neja karkashin jagorancin Gwamna Mohammed Umar Bago, na da nufin hada kai da muhimman masu ruwa da tsaki a fannin tsaro na matakin karamar hukuma, jiha da na tarayya, domin samo ingantacciyar mafita ga kalubalen tsaro a jihar.

 

Janar Bello Abdullahi, wanda ya bayyana kafafen yada labarai a matsayin muhimman masu ruwa da tsaki a yaki da rashin tsaro, ya jaddada cewa sai an hada kai gaba daya ne za a samu nasara.

 

A nasa jawabin, Shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa reshen Jihar Neja, Kwamared Abu Nmodu, ya jaddada cewa akwai bukatar gwamnati ta tantance tsakanin ‘yan jaridu na gaskiya da kuma na bogi, wanda hakan zai taimaka matuka wajen cimma nasarar da ake bukata a jihar, da kuma amfanin al’umma baki daya.

 

Sakataren yada labarai na Gwamnan Jihar Neja, Bologi Ibrahim, wanda Hamza Mohammed mai kula da harkokin yada labarai na Gwamna, ya wakilta, ya bukaci hadin gwiwa domin ci gaban jihar.

 

Taken taron zaman lafiya da tsaro na farko a Jihar Neja wanda za a gudanar gobe Laraba 20 ga watan Mayun 2025, shi ne: “Hadin Gwiwa Wajen Gina Tsaro da Zaman Lafiya Domin Kare Jihar Neja.”

 

Daga Aliyu Lawal

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe

Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.

Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.

Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a Borno

Da yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.

“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.

A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.

Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.

Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An Bude Dandalin Tattauna Batutuwan Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Beijing 
  • Larijani: Iran Da Saudiyya Za Su Bunkasa Aiki Tare A Fagagen Kasuwanci Da Tsaro
  • Tinubu ya janye dokar ta-ɓaci da ya sanya a Ribas
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Gwamnatin Neja Ta Musanta Rahoton Hana Da’awa A Jihar
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja