Gwamnatin Jihar Neja ta bayyana cewa ya zama wajibi ta yi duk mai yiwuwa don tabbatar da yaki da rashin tsaro a kafatanin kananan hukumomi ashirin da biyar na jihar

 

Kwamishinan Ma’aikatar Tsaron Cikin Gida na Jihar Neja, Birgediya Janar Mohammad Bello Abdullahi, ne ya bayyana hakan yayin da yake jawabi ga manema labarai a taron shirye-shiryen babban taron tsaro da za a gudanar a Minna.

 

Janar Mohammad Bello Abdullahi ya kara da cewa Gwamnati jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba wajen yaki da rashin tsaro, inda ya bukaci hadin gwiwa daga kowane bangare domin cimma burin da aka sanya a gaba.

 

A cewarsa, babban taron zaman lafiya da tsaro na farko da za a gudanar a Jihar Neja karkashin jagorancin Gwamna Mohammed Umar Bago, na da nufin hada kai da muhimman masu ruwa da tsaki a fannin tsaro na matakin karamar hukuma, jiha da na tarayya, domin samo ingantacciyar mafita ga kalubalen tsaro a jihar.

 

Janar Bello Abdullahi, wanda ya bayyana kafafen yada labarai a matsayin muhimman masu ruwa da tsaki a yaki da rashin tsaro, ya jaddada cewa sai an hada kai gaba daya ne za a samu nasara.

 

A nasa jawabin, Shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa reshen Jihar Neja, Kwamared Abu Nmodu, ya jaddada cewa akwai bukatar gwamnati ta tantance tsakanin ‘yan jaridu na gaskiya da kuma na bogi, wanda hakan zai taimaka matuka wajen cimma nasarar da ake bukata a jihar, da kuma amfanin al’umma baki daya.

 

Sakataren yada labarai na Gwamnan Jihar Neja, Bologi Ibrahim, wanda Hamza Mohammed mai kula da harkokin yada labarai na Gwamna, ya wakilta, ya bukaci hadin gwiwa domin ci gaban jihar.

 

Taken taron zaman lafiya da tsaro na farko a Jihar Neja wanda za a gudanar gobe Laraba 20 ga watan Mayun 2025, shi ne: “Hadin Gwiwa Wajen Gina Tsaro da Zaman Lafiya Domin Kare Jihar Neja.”

 

Daga Aliyu Lawal

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini

Majalisar Dokokin Amurka ya iso Abuja yayin da ƙasashen biyu ke ƙara matsa ƙaimi wajen tattaunawar diflomasiyya kan haɗin gwiwar tsaro da kuma zargin tauye haƙƙin addini.

Mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan tsaro Nuhu Ribadu, ya ce ya gana da wakilan kuma zuwan tawagar na cikin abubuwan da suka amince da shi a tasu ziyarar da suka kai birnin Washington a watan Nuwamba.

“Tawagar ta ƙunshi ‘yanmajalisar wakilai Mario Díaz-Balart, Norma Torres, Scott Franklin, Juan Ciscomani, da Riley M. Moore,” in ji Ribadu cikin wata sanarwa a shafinsa na sada zumunta.

Kazalika, Jakadan Amurka a Najeriya Richard Mills na cikin tawagar.

A cewar Ribadu, tattaunawar ta mayar da hankali kan yaƙi da ta’addanci, tabbatar da zaman lafiyar yanki da kuma ƙarfafa haɗin gwiwar tsaro tsakanin Nijeriya da Amurka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda muka daƙile yunƙurin juyin mulki a Benin — Sojin Saman Najeriya
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Ma’aikatar Ayyuka da Sufuri ta Jigawa Ta Bada Kiyasin Kasafin Kudi na Sama da Naira Biliyan 161
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa
  • Fyaɗe ga ’yar shekara 12 ya ja wa matashi ɗaurin rai-da-rai a Yobe
  • Jigajigan Majalisar Ribas 17 Sun Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
  • Akwai hannun ƙasashen waje a rashin tsaron Najeriya —Sheikh Gumi
  • Na kashe N100bn a kan harkar tsaro a 2025 — Zulum
  • Jami’an tsaro sun kama masu garkuwa da mutane 7 a Gombe
  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara