Ma’aikatar Cinikayya Ta Sin Ta Yi Karin Haske Game Da Soke Takunkumin Da Amurka Ta Kakabawa Sin
Published: 5th, July 2025 GMT
Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin ya amsa tambayoyin ‘yan jaridu, dangane da soke takunkumin tattalin arziki da cinikayya da kasar Amurka ta kakabawa kasar Sin.
Kakakin ya ce, bayan tattaunawar tattalin arziki da cinikayya da aka yi tsakanin kasar Sin da kasar Amurka a birnin London na kasar Burtaniya, cikin ’yan kwanakin nan, bangarorin biyu sun aiwatar da ra’ayi daya da shugabannin kasashen biyu suka cimma a ranar 5 ga watan Yuni, tare da inganta ayyukan da abin ya shafa bisa sakamakon da suka cimma a taron tattaunawar tattalin arziki da cinikayya na Geneva.
Da kyar bangarorin biyu suka cimma matsaya daya tare da kulla “tsarin London”, don haka ya kamata a bi hanyar yin shawarwari, maimakon kalubalanta ko tilastawa wani. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Harin Kan Cibiyar Makamashin Nukiliya Cin Amanar Diflomasiyya Ce
Ministan harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran cin amanar diflomasiyya ce
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana harin da sojojin Amurka suka kai kan cibiyoyin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya a matsayin cin amanar diflomasiyya da kuma cewa wani mataki ne da ba a taba ganin irinsa ba ga tsarin doka da hakkin kasa da kasa da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya.
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi da Ronald Lamola, ministan hulda da kasa da kasa da hadin gwiwa na Jamhuriyar Afirka ta Kudu, sun tattauna batutuwan baya-bayan nan da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya bayan dakatar da hare-haren soji da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka yi kan Iran a wata tattaunawa ta wayar tarho a ranar Laraba.
Araqchi ya bayyana jin dadinsa ga matsayin Afrika ta Kudu wajen yin Allah wadai da zaluncin sojin gwamnatin ‘yan sahayoniyya masu nuna wariyar al’umma suka dauka na kai wa kasar Iran hari, yana mai cewa: Hare-haren wuce gona da iri da gwamnatin ‘yan sahayoniyya ta dauka a kan Iran, sakamakon rashin hukunta ta ce da kuma gazawar kasashen duniya wajen mayar da martani kan laifukan da take aikatawa a Gaza da kuma hare-haren da take kai wa Lebanon da Siriya, kuma tabbas dukkanin masu goya mata baya suna da hannu wajen aikata laifukan da take aikatawa.
Ya yi nuni da cewa: Harin da sojojin yahudawan sahayoniyya suka kai wa Iran ya faru ne a cikin shawarwari da kuma goyon bayan gami da taimakon Amurka. Daga nan ne Amurka ta kaddamar da harin soji kan cibiyoyin nukiliyar Iran na zaman lafiya, tare da jaddada cewa matakin da Amurka ta dauka ya zama cin amanar diflomasiyya da kuma wani matakin da ba a taba ganin irinsa ba na rashin bin doka da oda, da take hakkin kasa da kasa, da kuma tsarin hana yaduwar makaman nukiliya.