Sojojin mamayar Isra’ila sun mayar da cibiyoyin bada agaji zuwa filin yakin kashe Falasdinawa a Zirin Gaza

Sojojin mamayar Isra’ila suna ci gaba da mayar da cibiyoyin bayar da agajin jin kai zuwa wani mummunan tarko na aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa, wanda hare-haren baya-bayan nan da suka kai kan fararen hula sunka yi sanadiyar hasarar rayuka da dama tare da jikkata wasu masu yawa.

Wannan mummunan al’amari ya janyo gargadin Majalisar Dinkin Duniya cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila tana kai wa masu fama da yunwa hari.

Jiragen yakin gwamnatin mamayar Isra’ila da kuma amfaniu da manyan bindigogi suna barin wuta kan mai uwa da wabi kan Falasdinawa da suka taru domin karbar kayan jin kai. Gwamnatin mamayar Isra’ila ta bullo da wannan sabon hanya ce domin kashe Falasdinawa a matsayin tarko ga Falasdinawa, kuma ba ta sha yin ci gaba da wannan ta’asa domin babu mai iya hana ta ko tofin yin Allah wadai da ita.

Wani magidanci da ya dawo daga karbar agaji da ‘ya’yansa biyu a Khan Yunus, ya fuskanci bude wuta inda dansa guda ya yi shahada dayan kuma yana nan rai kwai-kwai mutum kwai-kwai.

A cewar wata sanarwa da ma’aikatar harkokin cikin gida da tsaron kasa a zirin Gaza ta fitar, ta jaddada cewa: Daruruwan Falasdinawa ne suka yi shahada sakamakon harsashin sojojin mamayar Isra’ila a wuraren bada agajin jin kai zuwa yanzu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: mamayar Isra ila

এছাড়াও পড়ুন:

Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan

Kwamandan sojojin kasar Iran ya jaddada cewa: Sojojin Iran sun shirya tsaf don kare juyin juya halin Musulunci da kasarsu

A yayin ziyarar da ya kai wa iyalan shahidi kwamandan tsaron cikin gida na kasar Iran Kanal Mohammad Alizadeh; Babban kwamandan sojojin kasar Iran Manjo Janar Amir Hatami ya bayyana cewa: Jajirtattun sojojin kasar Iran a shirye suke da dukkanin karfinsu wajen kare kyawawan manufofin juyin juya halin Musulunci da kuma dukkanin yankin Jamhuriyar Musulunci ta Iran a cikin kowane irin yanayi da kuma fuskantar duk wani mai neman wuce gona da iri.

Manjo Janar Amir Hatami, babban kwamandan sojojin kasar Iran, tare da rakiyar Hujjatul-Islam Ahmad Jalili Safat, mataimakin shugaban bangaren rukunan siyasa ta sojojin kasar, Manjo Janar Muhammad Yousufi Khosh-Qalb, mataimakin kodinetan sojojin sama, da Hujjatul-Islam Muhammad Bahman, shugaban sashen siyasa na bangaren sojan sama, Muhammad Ali sun ziyarci gidan shahidi jajirceccen mayakin rundunar sojin saman Iran kanal Muhammad Ali Zadeh, inda suka gana da iyalan wannan shahidi mai girma tare da girmama matsayin daukakarsa na samu shahada.

A yayin wannan ziyarar, Manjo Janar Hatami ya mika sakon taya murnar shahadar narigayi da ta’aziyyar tashinsa, gami da tunawa da wannan shahidi daga rundunar sojojin sama da dukkan sauran shahidai masoya masu girma da suka sadaukar da kansu a lokacin wuce gona da irin da yahudawan sahayoniyya suka kawo hare-haren ta’addanci kan Iran. Yana mai jaddada cewa: Shahadan bayin Allah salihai a cikin wannan harin wuce gona da iri, ya nuna girman ta’addancin makiya masu dauke da ruhin zalunci, kuma lallai sun tarar da jajirtattun gwarazan Iraniyawa da suka sadaukar da kansu domin kare al’umma da kasarsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda da ƙwato makamai a Borno
  • Zanga-zangar ‘Yan Gudun Hijira Na Yelewata ‘Yar Manuniya Ce Ga Daukar Matakan Da Suka Dace
  •   Gaza: Fiye Da Falasdinawa 17 Ne Su Ka Yi Shahada Ayau Juma’a
  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Sake Aiwatar Da Kisan Kare Dangi Kan ‘Yan Gudun Hijiran Falasdinawa
  • Lukurawa Sun Kashe Mutane 15 a Sakkwato
  • Ben Gafir Ya Bukaci Gwamnatin HKI Ta Mamaye Yankin Gaza Gaba daya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Luguden Bama-Bamai Kan Falasdinawa Da Suka Janyo Shahada Da Jikkata
  • Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang