Ya misalta rashin basaraken da cewa, ba rashin ne kawai ga iyalai ko al’ummar masarautarsa ba, a’a rashi ne ga illahirin masarautar Bauchi da ma jihar Bauchi baki ɗaya.

 

Gwamna Muhammad ya misalta Alhaji Garba a matsayin babban basaraken gargajiya wanda aka sani da hikima, tawali’u, da sadaukar da kai ga hidimta wa al’ummarsa.

 

“Ya kasance mutum mai dattako wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen kyautata zaman lafiya da cigaba,” in ji gwamna Bala.

 

Gwamnan sai ya yi addu’ar Allah ya jiƙan mamacin ya gafarta masa kura-kuransa tare da sanya shi cikin aljanna maɗaukakiya. Ya kuma jajanta wa masarautar Bauchi, iyalai da al’ummar jihar da fatan Allah ba su haƙurin juriya na wannan babban rashin..

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

An tafka asara bayan gobara ta ƙone Kwalejin Sheikh Dahiru Bauchi

Gobara ta tashi a Kwalejin Karatun Alƙur’ani da ilimin addinin Musulunci mallakin fitaccen malamin nan, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, da ke Rafin Albasa, a Jihar Bauchi, inda ta ƙone ginin makarantar da kayan cikinta.

Binciken wakilinmu ya gano cewa gobarar ta lalata bene mai ɗakuna da dama ciki har da ofisoshi, ajujuwa, ɗakunan gwaje-gwaje, ɗakunan kwamfuta, da ɗakunan karatu.

Jami’in Sibil Difens ya mayar da N800,000 da wata Hajiya ta zubar a Adamawa Yadda ’ya’yan shugabanni ke musu yaƙi da ’yan adawa

An kuma rasa kayan sawa na malamai da ɗalibai, katifu, barguna da sauran kayayyakin amfanin yau da kullum.

Har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba.

Sai dai daraktan makarantar, Sayyadi Aliyu Sise Dahiru, ya ce sun gode wa Allah da ba a rasa rai ko samun rauni ba.

“Lamarin ya faru ne bayan an kammala karatu da yamma, kuma muna godiya ga jami’an kashe gobara da suka kwashe sa’o’i suna ƙoƙarin kashe wutar,” in ji shi.

Ya ce makarantar na da alaƙa da Jami’ar Azhar da ke ƙasar Masar, kuma tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Namadi Sambo ne ya ƙaddamar da ita.

A cewarsa, makarantar kwana ce da ke bayar da ilimin boko da na Islamiyya tare da koyar da sana’o’i.

Kowace shekara ana yaye mahaddatan Alƙur’ani da dama a makarantar.

Ya ce an rasa litattafan Sheikh Dahiru Bauchi da na sauran malamai da dama, ciki har da kwamfutoci da kayan aikin makaranta.

Hukumar kashe gobara ta Jihar Bauchi ta bayyana cewa gobarar ta ƙone littattafai kusan 7,228, suturar ɗalibai kusan 583, gadaje 250, darduma mai faɗin mita 355, kujerun cin abinci 324, katifu, jakunkuna, kayan girki da sauran muhimman takardu da hotuna guda 150.

Ana ci gaba da bincike don gano musabbabin tashin gobarar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara Ta Kafa Tutar Hadin Kai Mai Mita 70 A Ilorin
  • Kwamishina ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe
  • Kwamishiniya ta nemi a hukunta wanda ake zargi da yi wa ’yar matarsa fyaɗe a Gombe
  • Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15
  • Gwamna Abdulrazaq Ya Jajanta Wa Wadanda Hatsarin Jirgin Ruwan Gbajibo Ya Rutsa Da Su
  • Hajji: Gwamnatin Katsina ta biya wa maniyyata 2000 kuɗin hadaya
  • An tafka asara bayan gobara ta ƙone Kwalejin Sheikh Dahiru Bauchi
  • Gwamna Lawal Ya Ƙaddamar Da Ginin Babban Asibitin Anka Da Aka Inganta
  • Guguwar raba Masarautar Katsina ta kunno kai