Aminiya:
2025-07-05@01:34:26 GMT

Hadiman gwamnan Kano sun haura 300 bayan naɗa wasu sabbi 19

Published: 5th, July 2025 GMT

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da naɗin wasu sabbin hadimai 19 da za su yi aiki a matsayin Manyan Mataimaka na Musamman domin ƙara inganta aikin gwamnati a jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ne ya sanar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma’a.

Mai shekara 70 ya kashe ƙanwarsa kan gadon gona a Jigawa Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu

Yanzu adadin hadiman da ke aiki da Gwamna Abba sun zarce mutum 300.

Hadiman sun haɗa da Masu Ba da Shawara na Musamman, Manyan Mataimaka na Musamman, Mataimaka na Musamman da kuma Masu Taimaka Masa.

Gwamnan ya fara naɗa hadimansa ne a ranar 16 ga watan Yunin 2023, inda ya naɗa mutum 14 ciki har da Manyan Mataimaka bakwai, Mataimaka na Musamman uku da Masu Taimaka Masa guda huɗu.

Daga baya, a ranar 18 ga watan Yuli, 2023, ya sake naɗa ƙarin mutum 15 a matsayin Masu Ba da Shawara na Musamman.

A ranar 7 ga watan Agusta, 2023, ya sake naɗa mutum 52, wanda ya kai jimillar hadimansa zuwa 81 a wancan lokaci.

A ranar 2 ga watan Satumba, 2023, ya sake naɗa ƙarin mutum 115; waɗanda suka haɗa da Masu Ba da Shawara 14, Manyan Mataimaka 57 da Masu Ɗaukar Rahoto na Musamman 44.

Hakazalika, a ranar 27 ga watan Satumba, ya sake ƙara mutum 94, wanda ya adadin ya kai zuwa 290.

Bayan haka, a ranar 29 ga watan Satumba, 2023, ya ƙara naɗa mutum 106; ciki har da Manyan Mataimaka 63, Mataimaka na Musamman 41 da wasu 12.

Yanzu kuma, ya sake naɗa mutum 19, wanda adadin hadimansa ya haura 300.

Daga cikin sabbin waɗanda ya bai wa muƙamai akwai Hon. Sunusi Kata Madobi da aka naɗa a matsayin Mataimaki na Musamman Kan Harkar Gidan Rediyo na I domin maye gurbin marigayi Abdullahi Tanka.

Mika’ilu Shu’aibu (Ghari) ya zama Mataimaki na Musamman Kan Harkokin Hisbah, yayin da Muhktar Abdullahi Shuwaki (Ghari) ya zama Mataimaki na Musamman Kan Harkokin Filaye.

Injiniya Sagir Lawan Waziri (Ghari) ya samu muƙamin Mataimaki na Musamman Kan Hakkokin Al’umma (Sashen Ayyuka).

An naɗa Najeef Abdulsalam a matsayin Mataimaki na Musamman Kan Masu Sana’o’i Maza, sai kuma Huwaila Iguda da aka naɗa a matsayin Mataimakiya ta Musamman Kan Masu Sana’o’i Mata.

Naziru Hamidu Bako ya zama Mataimaki na Musamman Kan Hukumar KAROTA, sai Usman Abbas Sunusi da zai riƙe matsayin Mataimaki na Musamman Kan Harkokin Taruka na II.

Injiniya Usman Kofar Naisa zai kasance Mataimaki na Musamman Kan Filin Wasanni na Mahaha, yayin da Danladi Alhassan Mai-Bulala ya zama Mataimaki na Musamman Kan Wayar da Kai II.

Abdulkhadir Umar Kwankwaso ya samu muƙamin Mataimaki na Musamman Kan Harkar Ilimi (Abuja), sai kuma Balarabe Aminu Yusuf wanda aka daga darajarsa zuwa Mataimaki na Musamman Kan Harkokin Gida III (Gidan Gwamnati).

Shukurana Garba Langel ya zama Mataimaki na Musamman Kan Wayar da Kai (Kano ta Arewa), sai Mustapha Ma’aruf Diso da aka naɗa Mataimaki na Musamman Kan Harkar Kiwon Lafiya A Matakin Farko (Primary Healthcare).

Garba Yahaya Labour ya zama Mataimaki na Musamman Kan Harkokin Sufuri na I, yayin da Humaira Sharif ta zama Mataimakiya ta Musamman Kan Wayar da Kan Mata.

Muttaka Sani Gaya, ya samu muƙamin Mataimaki na Musamman Kan Ƙungiyoyin Masu Goyon Bayan Gwamnati na III, Gausu Nuhu Wali ya zama Mataimaki na Musamman Kan Mawaƙan Gargajiya, sai kuma Hadiza Sale (Baby) da aka naɗa a matsayin Mataimakiya ta Musamman Kan Tsaftar Muhalli.

Gwamnatin Kano ta yi fatan sabbin hadiman za su yi amfani da ƙwarewarsu da kishinsu wajen taimakawa wajen cimma burin gwamnatin na mayar da hankali kan ci gaban jama’a da shugabanci na gari.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamnan Kano Mataimaki na Musamman Kan Harkokin ya zama Mataimaki na Musamman Kan a matsayin Mataimaki Manyan Mataimaka ya sake naɗa da aka naɗa naɗa mutum

এছাড়াও পড়ুন:

2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC

Jagoran sabuwar jam’iyyar ADC, Ralph Nwosu, ya bayyana cewa tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark, zai jagorance su wajen karɓar mulki daga hannun Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

Jam’iyyar haɗakar, wacce ta ƙunshi fitattun ’yan siyasa, ta naɗa David Mark a matsayin Shugaba, tare da tsohon Gwamnan Jihar Osun, Rauf Aregbesola, a matsayin Sakatare.

’Yan sanda sun kama wani mutum da jabun kuɗi a Gombe Ambaliya: Zulum ya bada umarnin tallafa wa mutanen Damboa da Askira-Uba

A wajen babban taron da ta gudanar a cibiyar Yar’Adua da ke Abuja, Nwosu ya ce: “Mun sauka daga muƙamanmu domin mu bai wa David Mark dama ya jagoranci wannan tafiya zuwa fadar shugaban ƙasa.”

Ya yaba wa Aregbesola, wanda ya taɓa kasancewa abokin siyasar Tinubu, inda ya ce mutum ne mai aiki tuƙuru da kishin ƙasa.

Nwosu ya ƙara da cewa: “’Yan Najeriya sun gaji. Sun ƙosa da sauyi. Wannan haɗaka da muke yi na da matuƙar muhimmanci.

“Ina goyon bayansa sosai, kuma ba zan huta ba har sai mun isa fadar shugaban ƙasa, mun rera taken ƙasa a can. Najeriya na cikin tsaka mai wuya.

“Rayuka na salwanta kullum. Shugabanninmu na gaba su fitar da Najeriya daga wannan halin, su kai ta ga ci gaba. Za mu iya!”

Ya kuma gargaɗi masu sukar wannan haɗakar da cewa ba ’yan jam’iyyar ADC ba ne.

“Babu buƙatar yin nadama a kan abin da muka yi yau. Wannan tafiya ce mai wahala, dole mu kasance a shirye.”

Daga cikin fitattun mutane da suka halarci taron har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar; ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi.

Sauran sun haɗa da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai; tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi; da tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, da sauransu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  • 2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC
  • Abba ya naɗa Ahmed Musa a matsayin Babban Manajan Kano Pillars
  • SON Ta Bada Shaidar Ingancin Kayayyaki Ga Wasu Kamfanoni A Kaduna
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 6, sun raunata wasu a Kwara
  • ’Yansanda Sun Ceto Ɗan Ghana, Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 3
  • ‘Mutum 600 da suka bace a ambaliyar Mokwa sun mutu’
  • 2027: David Mark zai kai mu ga nasara — ADC
  • DAGA LARABA: Cutukan Da Sinadaran Yin Burodi Ke Haifarwa