Aminiya:
2025-11-03@07:46:32 GMT

An kama malama tana lalata da ɗalibinta

Published: 16th, March 2025 GMT

An kama wata malamar makarantar sakandare ta California a Amurka da ake zargi da lalata da wani ɗalibi mai shekaru 17.

Wannan da ba shi ne karon farko ba da aka tuhumi wani da irin wannan hali ba a makaranatar.

Yadda ango da ’yar uwar amarya suka rasu minti 30 kafin ɗaurin aure a Bauchi Soja ya shafe mako guda da harsashi a cikin ƙwaƙwalwarsa

An kama malama Dulce Flores, mai shekara 28 bayan da ta kulla dangantakar da ba ta dace ba da wani dalibi dan shekara 17 a makarantar sakandare ta Riberbank a 2023, a cewar ’yan sandan Riverbank.

Malamar wacce take koyar da harshen Sipaniya tana aiki a makarantar tun 2016.

Haka kuma a cewar shafinta na LinkedIn, ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da shawara kan kyau ga wani kamfani na kayan kwalliya.

A wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar ta ce, an fara gudanar da binciken ne bayan wani jami’in makarantar ya samu labarin alakar malamar da dalibin.

An kama Flores a cikin gidanta, inda aka tuhume ta da laifin yin lalata da karamin yaro ba bisa ka’ida ba, in ji ‘yan sanda.

Gundumar makarantar a baya ta bayyana wa jaridar The Modesto Bee cewa, za su hada kai da masu bincike idan akwai bukatar hakan kuma sun bai wa Flores hutu har sai an gama gudanar da bincike.

Mahukuntan makarantar sun ci gaba da cewa, za su yi magana da iyaye da daliban da suka yi rajista a azuzuwan Flores.

A cikin wata sanarwa, Sufeto Constantio Aguilar ya ce: ‘Abin takaici ne ga gundumarmu ta fuskanci yanayi irin wannan.

Yayin da muke ci gaba da yin aiki tare da jami’an tsaro, gundumar kuma za ta duba don tantance irin matakan da za ta iya bi don magance lamarin.’

Gundumar ta kara da cewa, ba ta tsammanin komai sai mafi kyawun inganci da kwarewar ma’aikatansu.’

An tsare Flores a gidan yari na Stanislaus County da neman beli a kan Dalar Amurka 20,000 bayan da wakilin gundumar suka samu sammacin kama ta.

Ofishin gundumar yankin Sheriff ya gode wa mahukuntar makarantar sabda ‘ba da rahoto cikin gaggawa’ da hadin kai wanda ‘ya taimaka wa masu bincike don tantance yanayin lamarin.’

Har yanzu dai ba a tabbatar da halin da take ciki a gidan yari ba. Babu tabbas ko Flores za ta daukaka kara.

Wannan dai ba shi ne karon farko da aka kama wani ma’aikacin makarantar sakandaren Riverbank da laifin yin lalata da wani dalibi ba.

A shekarar 2023 makarantar sakandare ta Riverbank ta fada cikin irin wannan yanayi bayan da aka zargi wani tsohon kocin kwallon kwando mai shekara 23 a lokacin da yin lalata da wani matashi dan shekara 16.

Logan Navors na fuskantar tuhumetuhume da suka shafi lalata da karamin yaro.

An gurfanar da Navors a gaban kotu a watan Satumba, amma ba a sani ba ko ya daukaka kara a wannan lokacin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibi

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba

A 2022, kasashe shida ne suka daina yanke hukuncin kisa, ko dai gaba daya ko kuma wani bangare.

Hudu daga cikinsu; Kazakhstan, Papua New Guinea, Saliyo, Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, sun jingine shi kwatakwata.

Ekuatorial Guinea da Zambia sun ce za a rika amfani da shi ne kawai kan laifuka mafiya kololuwar muni.

A watan Afrilun 2023, majalisar dokokin Malaysia ta kada kuri’ar daina amfani da shi a matsayin tilas kan laifuka 11, ciki har da kisa da kuma ta’addanci.

Majalisar dokokin Ghana ma ta kada kuri’ar soke hukuncin kisa a watan Yulin 2023.

 

Wadanne kasashe ne suka fi yanke hukuncin kisa?

Kasashe 20 ne suka zartar da hukunbcin kisa a 2022, idan aka kwatanta da 18 da suka yi hakan a 2021.

Kungiyar kare hakki ta Amnesty International ta ce jimillar mutum 1,518 aka zartar wa hukuncin kisa a duniya, inda aka samu karin kashi 32 cikin 100. Sai dai ta ce hakikanin adadin ya zarta haka sosai saboda yadda kasashe ke boye batun.

Bayan China, Amnesty ta ce kasashen da suka fi kashe mutane a 2024 su ne Iran (972), da Saudiyya (345), da kuma Iraki (63). Su ne suka zartar da kashi 91 cikin 100 na duka kasashen duniya.

Ana yi wa China kallon kasar da ta zarta kowacce aiwatar da hukuncin kisa a duniya, amma ba a sanin hakikanin adadin mutanen, saboda gwamnati ba ta bayyana su.

Kasashen Koriya ta Arewa da Bietnam ma na amfani da hukuncin kisa sosai amma ba su bayyanawa a hukumance.

Amnesty ta ce ta samu rahoton zartar da hukuncin kisa a bainar jama’a akalla sau uku a 2022 a Iran.

Ta ce Iran din ta kashe akalla mutum biyar saboda laifukan da suka aikata a lokacin da suke kasa da shekara 18 da haihuwa.

Saudiyya ta kashe mutane mafiya yawa a duniya a 2022 cikin shekara 30.

Kasashe biyar; Bahrain, Comoros, Laos, Nijar, Koriya ta Kudu – su ne suka yanke wa mutane hukuncin kisa a 2022 bayan sun shafe tsawon lokaci ba su yi amfani da shi ba.

Duk da cewa adadin na raguwa a Amurka, amma ya karu a 2021, amma duk da haka ya yi kasa sosai idan aka kwatanta da shekarar 1999.

 

Mutum nawa aka kashe saboda safarar miyagun kwayoyi?

Amnesty International ta ce sama da kashi 40 cikin 100 na mutanen da aka zartar wa hukuncin kisa a 2024 saboda laifukan ta’ammali da miyagun kwayoyi ne.

A 2022, an kashe mutum 325 saboda laifukan da suka shafi miyagun kwayoyi. Kasashen da suka aikata hakan su ne:Iran 255 Saudiyya – 57 – Singapore – 11

A 2023, Singapore ta zartar da hukuncin kisa kan mace ta farko cikin shekara 20. A 2018 aka kama Saridewi Djaman da laifin safarar hodar ibilis.

 

Ta yaya kasashe ke zartar da hukuncin kisa?

Saudiyya ce kadai ta zayyana fille kai a matsayin hanyar aiwatar da hukuncin kisa a 2022.

Sauran hanyoyin sun hada da rataya, da allura mai guba, da kuma harbi da bindiga.

A watan Janairun 2024 jihar Alabama ta Amurka ta zartar wa wani mai laifin kisa Kenneth Smith hukuncin kisa ta hanyar amfani da iskar nitrogen gas.

Ya zama mutum na farko a duniya da aka zartar wa hukuncin ta irin wannan hanyar, a cewar cibiyar Death Penalty Information Center da ke Amurka.

Lauyoyin Mista Smiths sun ce salon da ba a taba gwadawa ba kafinsa “rashin imani ne”.

Alabama da wasu jihohin Amurka biyu ne suka amince da amfani da iskar gas din saboda kwayoyin da ake amfani da su wajen yi wa mutum allura mai guba ba sa samuwa cikin sauki.

 

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su November 2, 2025 Manyan Labarai Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Matar aure ta yanka wuyan mijinta, ta fasa masa ido da wuƙa a Neja
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Shin Mene Ne Matsalar Liverpool A Wannan Kakar?
  • Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza
  • MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida
  • Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa