An kama malama tana lalata da ɗalibinta
Published: 16th, March 2025 GMT
An kama wata malamar makarantar sakandare ta California a Amurka da ake zargi da lalata da wani ɗalibi mai shekaru 17.
Wannan da ba shi ne karon farko ba da aka tuhumi wani da irin wannan hali ba a makaranatar.
Yadda ango da ’yar uwar amarya suka rasu minti 30 kafin ɗaurin aure a Bauchi Soja ya shafe mako guda da harsashi a cikin ƙwaƙwalwarsaAn kama malama Dulce Flores, mai shekara 28 bayan da ta kulla dangantakar da ba ta dace ba da wani dalibi dan shekara 17 a makarantar sakandare ta Riberbank a 2023, a cewar ’yan sandan Riverbank.
Malamar wacce take koyar da harshen Sipaniya tana aiki a makarantar tun 2016.
Haka kuma a cewar shafinta na LinkedIn, ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da shawara kan kyau ga wani kamfani na kayan kwalliya.
A wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar ta ce, an fara gudanar da binciken ne bayan wani jami’in makarantar ya samu labarin alakar malamar da dalibin.
An kama Flores a cikin gidanta, inda aka tuhume ta da laifin yin lalata da karamin yaro ba bisa ka’ida ba, in ji ‘yan sanda.
Gundumar makarantar a baya ta bayyana wa jaridar The Modesto Bee cewa, za su hada kai da masu bincike idan akwai bukatar hakan kuma sun bai wa Flores hutu har sai an gama gudanar da bincike.
Mahukuntan makarantar sun ci gaba da cewa, za su yi magana da iyaye da daliban da suka yi rajista a azuzuwan Flores.
A cikin wata sanarwa, Sufeto Constantio Aguilar ya ce: ‘Abin takaici ne ga gundumarmu ta fuskanci yanayi irin wannan.
Yayin da muke ci gaba da yin aiki tare da jami’an tsaro, gundumar kuma za ta duba don tantance irin matakan da za ta iya bi don magance lamarin.’
Gundumar ta kara da cewa, ba ta tsammanin komai sai mafi kyawun inganci da kwarewar ma’aikatansu.’
An tsare Flores a gidan yari na Stanislaus County da neman beli a kan Dalar Amurka 20,000 bayan da wakilin gundumar suka samu sammacin kama ta.
Ofishin gundumar yankin Sheriff ya gode wa mahukuntar makarantar sabda ‘ba da rahoto cikin gaggawa’ da hadin kai wanda ‘ya taimaka wa masu bincike don tantance yanayin lamarin.’
Har yanzu dai ba a tabbatar da halin da take ciki a gidan yari ba. Babu tabbas ko Flores za ta daukaka kara.
Wannan dai ba shi ne karon farko da aka kama wani ma’aikacin makarantar sakandaren Riverbank da laifin yin lalata da wani dalibi ba.
A shekarar 2023 makarantar sakandare ta Riverbank ta fada cikin irin wannan yanayi bayan da aka zargi wani tsohon kocin kwallon kwando mai shekara 23 a lokacin da yin lalata da wani matashi dan shekara 16.
Logan Navors na fuskantar tuhumetuhume da suka shafi lalata da karamin yaro.
An gurfanar da Navors a gaban kotu a watan Satumba, amma ba a sani ba ko ya daukaka kara a wannan lokacin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ɗalibi
এছাড়াও পড়ুন:
An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
Antoni Janar na Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke birnin Yamai a Nijar, ya bayyana cewa an kama tsohon Ministan Harkokin Waje, Ibrahim Yacoubou, bisa zargin hannunsa a cikin wata aika-aika ta kisan kai domin yin tsafi.
A cewar Maazou Oumarou, lamarin ya samo asali ne daga wani binciken ’yan sanda da aka fara gudanarwa tun a ranar 29 ga Yuli, 2025.
KEDCO ya ƙaryata asibitin AKTH kan mutuwar majinyata saboda ɗauke wuta Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan NejaYa bayyana cewa, an soma gudanar da binciken ne dangane da yunƙurin kisa a wani yanki da ke wajen birnin Yamai, lamarin da ya kai ga cafke ababen zargin a garin Dosso.
Wani mutum mai suna Mahamadou Noura ne ya bayyana cewa shi ne ya yi yunƙurin kisan, tare da wasu kashe-kashe guda shida da ya aiwatar a baya, bisa umarnin wasu mutane, ciki har da tsohon ministan Ibrahim Yacoubou.
Mutumin ya shaida wa mahukunta cewa ya aikata hakan ne domin yin tsafi da gawarwakin, a madadin wasu mutane da suka haɗa da: Issa Ali Maiga da Ismael Morou Karama da Elhadji Bilya da kuma Issa Seybou Hama.
TRT ya ruwaito cewa tuni dai an cafke duk ababen zargin, yayin da Kotun Ɗaukaka Ƙarar ta umurci ’yan sanda da su ci gaba da bincike tare da ɗaukar ƙarin matakan da za su tabbatar da gaskiya.
Sanarwar ta ce: “Manufar wannan mataki na shari’a ita ce a tattara cikakken rahoto da ke ƙunshe da dukkan abubuwan da suka faru, sannan a miƙa shi ga ɓangaren gurfanarwa.”
Mai shigar da ƙara a ɓangaren gwamnati ya ce, la’akari da girman wannan lamari, wajibi ne a gudanar da bincike cikin gaggawa.
Haka kuma ya buƙaci al’umma da su mutunta ’yancin kotu tare da bayar da cikakken goyon baya domin fayyace gaskiya.
Ana iya tuna cewa, Ibrahim Yacoubou na daga cikin manyan jami’an da aka kama bayan juyin mulkin Nijar na ranar 26 ga Yuli, 2023, sai dai daga bisani an ba shi beli na wucin gadi a cikin watannin baya.