Aminiya:
2025-06-15@19:09:54 GMT

An kama malama tana lalata da ɗalibinta

Published: 16th, March 2025 GMT

An kama wata malamar makarantar sakandare ta California a Amurka da ake zargi da lalata da wani ɗalibi mai shekaru 17.

Wannan da ba shi ne karon farko ba da aka tuhumi wani da irin wannan hali ba a makaranatar.

Yadda ango da ’yar uwar amarya suka rasu minti 30 kafin ɗaurin aure a Bauchi Soja ya shafe mako guda da harsashi a cikin ƙwaƙwalwarsa

An kama malama Dulce Flores, mai shekara 28 bayan da ta kulla dangantakar da ba ta dace ba da wani dalibi dan shekara 17 a makarantar sakandare ta Riberbank a 2023, a cewar ’yan sandan Riverbank.

Malamar wacce take koyar da harshen Sipaniya tana aiki a makarantar tun 2016.

Haka kuma a cewar shafinta na LinkedIn, ta kuma yi aiki a matsayin mai ba da shawara kan kyau ga wani kamfani na kayan kwalliya.

A wata sanarwa da ‘yan sandan suka fitar ta ce, an fara gudanar da binciken ne bayan wani jami’in makarantar ya samu labarin alakar malamar da dalibin.

An kama Flores a cikin gidanta, inda aka tuhume ta da laifin yin lalata da karamin yaro ba bisa ka’ida ba, in ji ‘yan sanda.

Gundumar makarantar a baya ta bayyana wa jaridar The Modesto Bee cewa, za su hada kai da masu bincike idan akwai bukatar hakan kuma sun bai wa Flores hutu har sai an gama gudanar da bincike.

Mahukuntan makarantar sun ci gaba da cewa, za su yi magana da iyaye da daliban da suka yi rajista a azuzuwan Flores.

A cikin wata sanarwa, Sufeto Constantio Aguilar ya ce: ‘Abin takaici ne ga gundumarmu ta fuskanci yanayi irin wannan.

Yayin da muke ci gaba da yin aiki tare da jami’an tsaro, gundumar kuma za ta duba don tantance irin matakan da za ta iya bi don magance lamarin.’

Gundumar ta kara da cewa, ba ta tsammanin komai sai mafi kyawun inganci da kwarewar ma’aikatansu.’

An tsare Flores a gidan yari na Stanislaus County da neman beli a kan Dalar Amurka 20,000 bayan da wakilin gundumar suka samu sammacin kama ta.

Ofishin gundumar yankin Sheriff ya gode wa mahukuntar makarantar sabda ‘ba da rahoto cikin gaggawa’ da hadin kai wanda ‘ya taimaka wa masu bincike don tantance yanayin lamarin.’

Har yanzu dai ba a tabbatar da halin da take ciki a gidan yari ba. Babu tabbas ko Flores za ta daukaka kara.

Wannan dai ba shi ne karon farko da aka kama wani ma’aikacin makarantar sakandaren Riverbank da laifin yin lalata da wani dalibi ba.

A shekarar 2023 makarantar sakandare ta Riverbank ta fada cikin irin wannan yanayi bayan da aka zargi wani tsohon kocin kwallon kwando mai shekara 23 a lokacin da yin lalata da wani matashi dan shekara 16.

Logan Navors na fuskantar tuhumetuhume da suka shafi lalata da karamin yaro.

An gurfanar da Navors a gaban kotu a watan Satumba, amma ba a sani ba ko ya daukaka kara a wannan lokacin.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibi

এছাড়াও পড়ুন:

Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai

Aƙalla mutum 26 ne suka rasu sakamakon wasu sabbin hare-haren da aka kai wasu ƙauyuka a Jihar Binuwai.

Hare-haren sun faru ne a yankunan Ƙaramar Hukumar Makurdi da Katsina-Ala tsakanin ƙarfe 12 na dare zuwa 2 na daren ranar Alhamis.

Farashin fetur ya tashi a kasuwar duniya bayan harin Isra’ila a Iran An kashe masu garkuwa da mutane da kuɓutar da wasu

A Ƙaramar Hukumar Makurdi, wasu ’yan bindiga sun kai hari ƙauyukan Mtswenem da Akondotyough Bawa, inda suka kashe mutum 25.

Haka kuma, an kashe mutum ɗaya a wani hari daban da aka kai ƙauyukan Kenvanger da Agbami a Ƙaramar Hukumar Katsina-Ala.

Wasu mazauna yankin sun ce ’yan bindigar sun shiga gidajen mutane suna harbin su yayin da suke barci, suna amfani da bindigogi da adduna.

Wani wanda ya tsira mai suna Iorpuu, ya ce mata da yara suna cikin waɗanda aka kashe, kuma har yanzu ana neman wasu da suka ɓace.

Ya ƙara da cewa wasu sun mutu ne a kan hanyarsu ta zuwa asibiti.

Wani ganau ya ce an fara kai harin ne wani ƙauye kusa da Jami’ar Noma da Fasaha ta Makurdi, inda aka kashe mutane huɗu.

Daga nan suka wuce wani ƙauye a kusa da unguwar Low Cost suka ci gaba da kashe mutane har adadin gawarwakin ya kai 25.

A Katsina-Ala, ’yan bindigar sun kai hari ƙauyukan Kenvanger da Agbami da misalin ƙarfe 1 na dare.

An ce sun yi yunƙurin yi wa wasu matan da suka haihu fyaɗe, amma mazan ƙauyen suka kai musu ɗauki.

Wannan ya haifar da rikici inda ’yan bindigar suka buɗe wuta, suka kashe mutum ɗaya tare da raunata wasu.

A ƙauyen Agbami kuma, sun yi wa mutane da yawa dukan kawo wuƙa amma babu wanda ya mutu.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Udeme Edet, ya tabbatar da cewa an tura jami’an tsaro zuwa yankunan da abin ya faru a Makurdi.

Ya ce za su ci gaba da bai wa ’yan jarida bayanai, amma har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, babu wani ƙarin bayani.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun IRGC Sun Kakkabo Jirahen Yakin HKI Wadanda Ake Sarrafasu Daga Nesa A Lardin Zanjan
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 100 a Benuwe
  •   Iran  Kakkabo Wani Jirgin Yakin HKI Samfurin F-35  Karo Na 3 Tare Da Kama Matukinsa
  • Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Afirka Sun Yi Alkawarin Karfafa Alaka
  • Mutum ɗaya ya tsira da ransa cikin 242 a hatsarin jirgin India