Ramadan Iftar: Sarkin Kauru Ya Hori Al’umma Su Hada Kai Su Zauna Lafiya da Juna
Published: 16th, March 2025 GMT
Mai Martaba Sarkin Kauru dake Jihar Kaduna Alhaji Zakari Ya’u Usman ya bukaci samun hadin kai da aiki tare kana da hakuri da juna tare da ɗaukar banbance banbance dake tsakanin al’umma a matsayin wata baiwa.
Alhaji Zakari Ya’u II yayi wannan horonne lokacin da aka taru a fadarsa dake Kauru domin shan ruwan azumin Ramadan.
Mai martaban ya bayyanawa wadanda suka taru domin wannan aikin lada na shekara shekara cewa, akwai bukatar yafiya da ‘yan uwantaka a wannan lokaci na Ramadan tare da godiya ga Allah da ya sake nuna mana wannan watan mai albarka.
Alhaji Zakaria Ya’u Usman yace akwai bukatar sadaukarwa da mika wuya ga Allah da kankantar da kai tare da fahimtar cewa wannan banbanci da ke tsakanin al’umma wata baiwa ce daga huwallazi tare da kira ga jama’a su nuna godiya ga Allah da wannan baiwar.
Yace Allah baya kuskure, saboda haka mu dauki wannan banbancin dake tsakanin mu a matsayi wata hanya ta aiki tare da nuna karfin mu na zama al’umma daya.
Sarkin Kauru ya godewa gwamnan jihar Kaduna Uba Sani saboda samarda zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Kaduna tare da gamsuwa da yunkurin karamar hukumar Kauru da jami’an tsaron wajen samar da kwanciyar hankali musamman kalubalen tsaron da wasu miyagun mutane suke haddasa wa a yankin.
Ganin yadda bukukuwan sallah ke karatowa, mai martaba ya hori talakawansa su kasance masu riko da kyawawan dabi’u da yafewa juna tare da tunatar da su cewa watan Ramadan ba wai ana magana akan azumi ne kadai ba, akwai bukatar ganin sa a ayukkan mu na yau da kullum.
Haka Kuma, sakataren masarautar Muhammad Sani Suleiman (Dan Buran Kauru) ya nanata kudurin masarautar na samarda zaman lafiya da hadin kai tsakanin al’ummar yankin.
Radio Nijeriya Kaduna ya bada labarin cewa an kammala wannan bikin shan ruwa na masarautar Kauru da gudanar da addu’o’in samun zaman lafiya da ci gaban al’ummar yankin a daidai lokacin da ake shirin bukukuwan sallah.
Yusuf Zubairu Kauru
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ramadan Iftar Sarkin Kauru Zauna Lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.
A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — DalungSanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.
“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”
Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.
Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.
Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.