Halayen Kirki 14 Da Ake Bukata Daga Malamin Makaranta (3)
Published: 16th, March 2025 GMT
12.Yadda a zahiranci abubuwa suke
A shekarar 2006,Carol Dweck wani masanin yadda mutum mai hankali yake,ya san yadda halin mutum yace a cikin littafinsa mai suna “rayuwar mutum da yadda hankalinsa yake” da wasu halayen da aka sa suke a littafinta.” mai suna:The Psychology of Success ko kuma hanyoyin da ake bi ko amfani da su domin a samu dama ta cimma nasara.
13. Ka iya tunkarar duk yadda dalibi yake
Dalibai da z aka koyar a matsayinka na Malamain su suna iya ko maganar gaskiya kowane daga cikin su akwai irin renon daya samu ta harkar ilimi kasancewarsu daga wurare daban daban, nau’oin dabarun da suke da sun a yin abubuwa,ga kuma matsaloli, dole ne kuma ka kwana cikin shirin lalle sai ka sadu da su duk kuwa da irin mizanin da suka cimmawa wwajen koyo.Wannan yana nufin ka tabbatar da kana da badara ko basirar da zaka iya tafiya da koyar da dalibai wadanda dabarar da ko salon da aka yi amfani da su wajen koya masu ya sha bamban dana saura duk a cikin aji daya ko kuma kungiya daya.Nan wani wuri ne inda wadansu abubuwa kamar a iya tafiya da irin halin da aka tsinci kai,ko lamarin tausayi, hakuri, wurin da za su aiki ko amfani ke nan ga su ma’abota ilimi.
14.Samun bambancin yadda aka koyar da daliban da suka bambanta da juna
Idan aka tattara ko tattaro abubuwa mabambanta akan darussa da kuma irin nau’in darussa da kuma sassan ko bangarori hakan yana nunawa dalibai yadda harkoki suke tafiya, da kuma aikin yadda ake maganin matsala yake in ana magana ta babu wasu boye- boye ne, yadda lamarin rayuwar yake a bayyane.
Idan har aka ce shi Malami ko kai Malami duk baka ko baka mallaki dukkan halayen kirki wadanda ake bukatar Malamin makaranta ya kasance yana da su ba,ba damuwar kanka o tada hankalinka zaka yi ba, ka sa a ranka cewar akwai wadansu abubuwan da suka kunshi su halayen inda zaka iya karuwa da su ta hanyar yin gwaji wadda ba mai wata wuya ba ce.Ko dai ta kasance kai babbar manufarka bata wuce ka samu damar ba wadanda basu da lakar fasaha ko wayo ba su kasance su farka daga barcin daya dauke su yayin da su kuma masu kwazon an kara masu kaimi,ko kuma su samu ko a koya masu sabbin dabaru masu kaifi sosai,takardar shedar ilimi ta digiri ko wadda bata kai hakan ba, wata dama ce ta mallakar shi ilimin da kwarewar da kai Malami kake bukata domin ka samu cimma burinka na abinda ka sa gaban sai ka kai can makura ko gaba da ita.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Rawar da Arewa za ta taka a Zaɓen 2027
’Yan siyasar yankin Arewa na ganin dole sai da goyon bayansu ɗan takara zai yi nasara a zaben Shugaban ƙasa.
Hakan na zuwa ne bayan tsohon maitaimaka wa shugaban ƙasa a fannin siyasa, Alhaji Hakeem Baba-Ahmed ya yi wata hira, inda yake cewa, nan da wata shida yankin zai fitar da matsayarsa.
An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas Dalilin da manyan ’yan siyasa ke barin NNPP — APCDuk da cewa Hakeem ba shi ne mai magana da yawun al’ummar yankin ba, amma ana kallon sa a matsayin daya daga cikin manya a yankin, saboda tsohon matsayinsa na mai magana da yawun Kungiyar Dattawan Arewa (NEF).
Tsarin siyasar kasar nan ya sa dole ne kowane dan takara ya zaga kowane lungu da sako na kasar nan kafin ya iya samun kuri’un da yake bukata don ya samu nasara.
Masana harkokin siyasa na ganin kalaman na Hakeem da ire-irensa na kan hanya, amma idan aka cika sharadi daya kacal.
“Rawar da Arewa za ta taka a zaben 2027 ba ta da wani bambanci da wadda ta saba takawa, kuma hakan zai yiwu ne kawai idan ta ci gaba da zama dunkulalliya, mai alkibla daya,” in ji Malam Kabiru Sufi na Kwalejin Share Fagen Shiga Jami’a ta Jihar Kano.
Idan dai aka cika wannan sharaɗi, to duk wani ɗan takara ko datn Arewa ne sai ya nemi goyon bayan ‘yan Arewacin kafin ya yi nasara.
Ya bayar da misalin haɗakar da jam’iyyun siyasa suka yi kafin babban zaben 2015, inda jam’iyyun CPC da ACN da ANPP da wani ɓangare na APGA da wasu gwamnonin PDP suka kafa APC mai mulkin.
“Idan aka samu rarrabuwar kai kuma, to Arewa za ta zama kamar wani taron tsintsiya ne ba shara. Babu rawar da za ta taka”, in ji Sufi.
Malam Sufi ya ce ɗaya daga cikin dalilan da suka sa ‘yan Arewa ke jin cewa sai da su za a ci zaɓe shi ne yawan al’umma.
A zaɓen 2023 da ya gabata, sahihan kuri’un da ‘yan takara huɗun farko suka samu a jihohin Arewa sun zarta na Kudu da kusan miliyan biyar.
Bola Ahmed Tinubu na Jam’iyyar APC da Alhaji Atiku Abubakar na PDP da Mista Peter Obi na LP da Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso na NNPP, sun samu jimillar kuri’u miliyan 13,716,667 a jihohin Arewa. Sun samu jimillar 9,020,741 a jihohin Kudu.
Bola Tinubu da ya lashe zaɓen ya samu jimillar 5,346,404 a jihohin Arewa, yayin da ya samu 3,206,969 a jihohin Kudu.
“In dai Arewa ta sake yin abin da ta yi a 2015, tabbas dole ne sai an nemi goyon bayanta, amma idan aka samu rarrabuwar kai za ta zama mushen gizaka – ana yi mata kallon za ta iya, amma kuma ba za ta iya ba,” kamar yadda Sufi ya bayyana.
Shin ko Arewan za ta iya magana da murya ɗaya?
Farfesa Abubakar Ma’azu, masanin harkokin siyasa ne a Jami’ar Maiduguri yana ganin za ta iya yin hakan.
“Idan aka duba, wadanda suka kafa Jam’iyyar APC sun fara yunkurin ne tun a 2011.
“Abin bai yiwu ba, amma suka shiga zabe a haka kuma suka sha kaye. Sai daga baya suka gano kuskurensu kuma suka yi nasara a 2015 bayan cim ma hadakar,” in ji shi.
Ko zai yiwu a iya cin zabe da kuri’un Arewa kawai? Kamar yadda ’yan Arewa ke tutiya da cewa sai da goyon bayansu za a ci zaɓen Shugaban ƙasa, haka ma sai dan takara ya samu kuri’u a Kudanci kafin ya yi nasara.
Kafin hadakar APC ta kayar da PDP mai mulki, tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi takara har sau uku ba tare da nasara ba, har sai bayan da ya samu goyon bayan wasu jam’iyyu daga Kudu.
Buhari ya fara yin takara ce a Jam’iyyar APP a 2003, ya sake yi a 2007 a jam’iyyar bayan ta zama ANPP, sai a 2011 kuma ya yi a CPC.
Ana ganin shigar Jam’iyyar ACN ta Bola Tinubu cikin haɗakar APC ce ƙashin bayan nasarar Buhari, saboda yadda take da tasiri a jihohin Kudu maso Yamma da Yarabawa ke da rinjaye.
Kazalika, Atiku Abubakar na Jam’iyyar PDP a zaben 2023 ya samu kuri’u mafiya yawa a Arewaci (4,834,767) sama da kudanci (1,751,047), amma duk da haka bai yi nasara ba.
“Dole ne sai ɗan takara ya karaɗe ƙasa baki ɗaya, ya samu kuri’u a Kudu da Arewa kafin ya samu kowace irin nasara,” in ji Farfesa Ma’azu.