INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12
Published: 5th, July 2025 GMT
“A wasu lokutan, ana cajin kudi masu yawa waje tallace-tallace. Wadannan abubuwan na cikin rashin bin doka a cikin dokar zabe ta 2022 wadda ke hana amfani da matsayi don musguna wa kowanne jam’iyya ko dan takara.
“Hukumarmu za ta yi aiki tare da cibiyar hadakar jam’iyyu (IPAC), kuma za mu kara karfafa hadin gwiwarmu da hukumar kula da tallace-tallace ta Nijeriya (ARCON), don daukar matakin doka idan aka samu shaidu masu karfi na karya doka.
“Game da zaben cike gibi kuwa, bari in ba ku takaitaccen bayani kan lamarin. A cikin shekaru biyu da suka gabata tun lokacin kaddamar da majalisun kasa da na jihohi a watan Yunin 2023, an samu kujerun ‘yan majalisa da babu kowa wanda ake bukatar yi zabe a fadin kasar nan.
“Idan za ku iya tunawa cewa a watan Fabrairu na shekarar da ta gabata, hukumar ta gudanar da zaben cike gurbi domin cike kujeru guda tara da aka samu sakamakon mutuwar ko murabus na ‘yan majalisun tarayya na jihohi. Tun daga wannan lokacin, an samu karin gurabe a fadin kasar nan.
“A saboda haka, hukumar ta fitar da ranar Asabar, 16 ga Agusta, 2025, don gudanar da zaben cike gibi a mazabu 16 a da ke jihohi 12 na kasar nan, wanda ya kunshin adadin masu zabe 3,553,659 da aka yi wa rajista, wanda aka rarraba a cikin kananan hukumomi 32, wuraren zabe 356 da kuma rukunin zaben 6,987. Hukumar za ta tura jami’ai 30,451,” in ji shugaban INCE.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
Kotun Babban Majistare da ke Yaba ta bayar da umarnin a tono gawarwakin mutane 10 da gobara ta kashe a ginin Afriland Towers da ke Legas a ranar 16 ga Satumba, 2025, domin a gudanar da bincike a kansu.
Alkalin kotun, Mai shari’a Atinuke Adetunji ce ta bayar da umarnin a ranar Talata bayan ta samu labarin cewa an riga da binne wasu daga cikin waɗanda gobarar ta ritsa da su.
“Mai ƙorafi ya rubuta wa Gwamnatin Jihar Legas don neman izinin tono gawarwakin waɗanda suka mutu, sannan a gudanar da bincike a kansu,” in ji Mai Shari’a Adetunji.
Wannan umarni ya biyo bayan wata wasiƙa daga ofishin babban lauya Femi Falana da aka aike wa Babban Mai Kula da Gawarwaki na Jihar Legas, Mai Shari’a Mojisola Dada, a ranar 29 ga watan Satumba, 2025.
Femi Falana (SAN), ta hannun ofishinsa, ya shigar da ƙorafi ga Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Legas, yana neman a gudanar da binciken gawarwaki don gano musabbabin mutuwar da kuma tabbatar da adalci.
A zaman farko na shari’ar, Mai Shari’a Adetunji ta umurci dukkan ɓangarorin da suka halarta da su gabatar da takardun da suka dace kafin zaman kotun na gaba.
Kotun ta kuma gayyaci hukumomi da kamfanoni da suka haɗa da bankin UBA da Hukumar Tara Haraji ta Tarayya (FIRS), Ma’aikatar Kashe Gobara, Afriland Towers, United Capital, Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Legas (LASEMA), Hukumar Tsaro ta Jihar Legas, da sauran masu ruwa da tsaki.
Adetunji ta ƙara da umartar mai ƙorafi da ya tuntubi iyalan waɗanda suka mutu don gano waɗanda ke da niyyar a tono gawar ’yan uwansu domin a gudanar da binciken gawarwaki.
Ta kuma nemi shaidun gani da ido da su bayyana don bayar da bayani kan abin da ya faru.
Lauya Yahaya Atata daga ofishin Falana ya shaida wa kotu cewa zaman na ranar an shirya shi ne don haɗa dukkan masu ruwa da tsaki da kuma fayyace yadda za a gudanar da binciken gawarwaki.
Sai dai alkalin ta lura cewa lauyoyin ba su shirya sosai ba, kuma ta jaddada cewa binciken ba zai ci gaba ba sai an gabatar da dukkan takardun da ake bukata.
Wani lauya mai wakiltar ɗaya daga cikin waɗanda suka mutu, A. O. Mema, ya shaida wa kotu cewa abokinsa, Peter Ifaranmaye, wanda shi ne manaja a Hukumar Tara Haraji ta Tarayya, an riga da binne shi.
Bayan wannan bayani, alkali Adetunji ta jaddada cewa yin binciken gawarwaki yana da matuƙar muhimmanci.
“Binciken gawarwaki muhimmin abu ne. Ba za mu iya gudanar da bincike ba sai an yi bincike don a gano hakikanin abin da ya faru,” in ji ta.
Kotun ta dage ci gaba da shari’ar zuwa ranar 26 ga watan Nuwamba, 2025.
Gobarar ta tashi ne a ginin Afriland Towers, wani katafaren ginin kasuwanci da ke titin Broad a unguwar Legas Island, a ranar 16 ga watan Satumba, inda ta kashe akalla mutane 10 tare da jikkata wasu da dama.
Shaidu sun ce gobarar ta fara ne da sassafe, kuma ta bazu cikin ginin da sauri kafin hukumomin kasha gobara su samu damar shawo kanta.