Shugaban kwamitin kungiyar tarayyar kasashen Afirka ta AU Mahamoud Ali Yousouf ya yabawa dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kungiyar AU cewa, kasar Sin a matsayin aminiya ce da za a iya dogaro da amincewa da ita.

A yayin da yake karbar takardar wakilcin kasa daga sabon shugaban tawagar jakadun kasar Sin dake kungiyar AU Jiang Feng, Mahmoud Yousouf ya bayyana cewa, kungiyar AU tana son karfafa mu’amala da hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin, domin samar da tabbaci ga kasashen duniya dake fama da sauye-sauye a halin yanzu.

A nasa bangare kuma, Jiang Feng ya mika gaisuwa da fatan alheri na shugabannin kasar Sin ga shugaba Yousouf, ya kuma yaba wa kungiyar AU bisa babbar gudummawar da ta bayar ga aikin shimfida zaman lafiya da zaman karko a nahiyar Afirka, da jagorantar dunkulewar kasashen Afirka, da kuma yin kira da a nuna adalci ga kasashen Afirka da sauransu. Haka kuma, ya ce kasar Sin tana son hada kai da kungiyar AU wajen aiwatar da sakamakon da aka cimma a taron koli na dandalin tattauna hadin gwiwar Sin da Afirka na Beijing, tare da gina makomar al’ummomin Sin da Afirka ta bai daya. (Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: kungiyar AU

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu

Gwamnan Jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya ƙaddamar da wani babban kwamitin ƙirƙiro masarautu da gundumomin hakimai a jihar.

An ƙaddamar da kwamitin ne a wani mataki na magance buƙatu da dama daga al’ummomi daban-daban da kuma inganta al’adu da tsarin mulki na asali a faɗin Jihar Bauchi.

Abba ya naɗa Ahmed Musa a matsayin Babban Manajan Kano Pillars An gano wasu bama-bamai 56 da ISWAP suka binne a Borno

Gwamna Bala ya shaida wa kwamitin da ya sake duba buƙatu na samar da sabbin masarautu a faɗin jihar.

Ya ce, aikin kwamitin shi ne inganta harkokin gudanar da mulki na cikin gida da inganta al’adu da kuma ƙarfafa muhimmiyar rawar da sarakuna ke gudanarwa wajen haɗin kai da ci gaba.

Gwamnan ya bayyana matakin a matsayin alƙawarin da gwamnatinsa ta yi na tabbatar da adalci da haɗa kai da kuma ƙarfafa tsarin mulki da ci gaba a Jiha da ƙananan hukumomi.

Ya bayyanawa kwamitin da ya ba da shawarar al’ummomin da suka cancanta na sabbin masarautu, da ba da shawarar tsarin gudanarwa don ingantaccen aiki na sabbin masarautu, masarautu ko gundumomi da gabatar da cikakken rahoto tare da shawarwari masu dacewa cikin makonni takwas.

Gwamnan ya buƙaci kwamitin da ya gudanar da aikinsa cikin gaskiya da himma da kuma adalci.

Ya bayyana cewa, shirin na cika alƙawuran siyasa ne da nufin karkatar da hukumomi don samar da ingantattun ayyuka da kuma ƙara rarraba albarkatu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Fira Ministan Pakistan Tare Da Tattaunawa Kan Harin Da Iran Ta Fsukanta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Rattaba Hannu Kan Daftarin Dakatar Da
  • Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu
  • Shugaban Amurka Yace Yana Jirin Hamas Cikin Sa’o’i 24 Masu Zuwa Don Tsagaita Wuta Na Kwanaki 60
  • Kayayyakin Sin Sun Kara Baiwa Masu Sayayya Na Kasa Da Kasa Damar Samun Zabi
  • Firaministan Sin Zai Halarci Taron Shugabannin Kasashen BRICS Na 17 A Brazil Da Kuma Ziyarar Aiki A Masar
  • Sin Na Ci Gaba Da Cika Alkawarin Bude Kasuwarta Ga Duniya
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Irin Aniyar Da Gwamantinsa Ta Kudurta Wajen Kare Tsaron Kasa Da Al’ummarta