Matashi ya kashe mahaifinsa da sanda a Jihar Bauchi
Published: 5th, July 2025 GMT
’Yan sanda sun kama wani matashi mai mai shekara 24 kan zargin ya kashe mahaifinsa mai shekaru 70 a ƙauyen Uzum da ke Ƙaramar Hukumar Giade ta jihar Bauchi.
Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce matashin ya yi amfani da sanda ne ya bugi mahaifin nasa a kai, nan take dattijon ya faɗi ya mutu.
Wani mazaunin ƙauyen Uzum da ke Giaɗe ya ce ake zargin ya lakaɗa wa mahaifinsa duka ne da sanda yayin da suke taƙaddama a gida da misalin karfe 10:30 na daren ranar Alhamis din da ta gabata.
Ya ce, “Ba mu san abin da ya faru ba, amma dai mun ji wata babbar hayaniya tsakaninsu, lamarin da ya sa shi ya bugi mahaifinsa da sanda a kai, mahaifin ya faɗi a sume.
Mai shekara 70 ya kashe ƙanwarsa kan gadon gona a Jigawa Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu“Mun sanar da ’yan sanda suka zo suka kai shi Babban Asibitin da ke Giaɗe, inda wani likita ya tabbatar da rasuwarsa da isar sa asibitin.”
Wakil ya bayyana wa manema labarai a ranar Juma’a a Bauchi cewa a ranar Alhamis da dare ne wani mutumin kirki ya kira su a ranar ya sanar da su.
Ya ce, “Da samun labarin kwamishinan ’yan sandan jihar Sani Omolori ya umurci jami’in ’yan sanda (DPO) da ke kula da Ofishin Shiyyar Giaɗe da ya gudanar da bincike domin gano ainihin abin da ya faru.
“Jami’an ’yan sanda sun je wurin da lamarin ya faru inda suka sami marigayin a kwance jina-jina, suka kai Babban Asibitin Giaɗe kuma likitan ya tabbatar da cewa ya rasu. An kuma miƙa gawarsa ga iyalansa domin yin jana’izarsa kamar yadda shari’ar Musulunci ta tanada.”
Ya ci gaba da cewa rundunar tana ci gaba da gudanar da bincike, babban wanda ake zargin kuma yana hannun ’yan sanda kuma bayan an kammala bincike za a gurfanar da shi a gaban kotu.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Sanda Sun Hana Yunqurin Fasa Shago a Gombe, Tare da Kwato Babur
Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Gombe ta hana yunqurin fasa wani shago da wasu vata-gari suka yi qoqarin yi a Unguwar Buba Shongo da ke cikin birnin Gombe, inda ta qwato wani babur da kayan da ake zargin an yi niyyar amfani da su wajen fasa shagon.
A cewar sanarwar da mai Magana da Yawun Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, lamarin ya faru ne da misalin qarfe 3:00 na safiyar Litinin, 1 ga Watan Yuli, 2025, lokacin da jami’an Operation Hattara ke kan sintiri a daren.
Jami’an sun hango wasu mutane da ba a san ko su wane ne ba suna qoqarin fasa wani shago mallakin wani Muhammadu Adamu Musa, mai shekara 42 da haihuwa.
Da vatagarin suka hango motar sintirin ‘yan sanda na qaratowa, sai suka tsere suka bar shagon ba tare da cimma burinsu ba.
Kayan da aka samu a wurin sun haxa da baqin babur qirar Yamaha mai lamba GME 480 VN da wani qarfe na tanqwara qoafa da takalmin roba guda xaya.
“Dukkan kayan da aka qwato suna hannun ‘yan sanda, kuma bincike yana ci gaba a kan zargin haxa baki da yunqurin aikata laifi,” in ji sanarwar.
Rundunar ta bayyana cewa wannan lamari ya qara tabbatar da cewar dokar da ta takaita zirga-zirgar babura a cikin dare a faxin jihar na nan daram, domin yawan laifukan da ake aikatawa da su a wannan lokaci na dare.
Rundunar ta kuma tabbatar wa da jama’a cewa tana ci gaba da qoqari don kamo waxanda suka gudu tare da gurfanar da su a gaban shari’a.
Haka zalika, rundunar ta buqaci jama’a da su kasance masu lura da abin da ke faruwa a muhallansu tare da ci gaba da bayar da sahihan bayanai ga jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da kare rayuka da dukiyoyin al’umma