Aminiya:
2025-10-16@11:46:19 GMT

Matashi ya kashe mahaifinsa da sanda a Jihar Bauchi

Published: 5th, July 2025 GMT

’Yan sanda sun kama wani matashi mai mai shekara 24 kan zargin ya kashe mahaifinsa mai shekaru 70 a ƙauyen Uzum da ke Ƙaramar Hukumar Giade ta jihar Bauchi.

Jami’in Hulɗa da Jama’a na rundunar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce matashin ya yi amfani da sanda ne ya bugi mahaifin nasa a kai, nan take dattijon ya faɗi ya mutu.

Wani mazaunin ƙauyen Uzum da ke Giaɗe ya ce ake zargin ya lakaɗa wa mahaifinsa duka ne da sanda yayin da suke taƙaddama a gida da misalin karfe 10:30 na daren ranar Alhamis din da ta gabata.

Ya ce, “Ba mu san abin da ya faru ba, amma dai mun ji wata babbar hayaniya tsakaninsu, lamarin da ya sa shi ya bugi mahaifinsa da sanda a kai, mahaifin ya faɗi a sume.

Mai shekara 70 ya kashe ƙanwarsa kan gadon gona a Jigawa Gwamnan Bauchi ya ƙaddamar da kwamitin ƙirƙiro da sabbin masarautu

“Mun sanar da ’yan sanda suka zo suka kai shi Babban Asibitin da ke Giaɗe, inda wani likita ya tabbatar da rasuwarsa da isar sa asibitin.”

Wakil ya bayyana wa manema labarai a ranar Juma’a a Bauchi cewa a ranar Alhamis da dare ne wani mutumin kirki ya kira su a ranar ya sanar da su.

Ya ce, “Da samun labarin kwamishinan ’yan sandan jihar Sani Omolori ya umurci jami’in ’yan sanda (DPO) da ke kula da Ofishin Shiyyar Giaɗe da ya gudanar da bincike domin gano ainihin abin da ya faru.

“Jami’an ’yan sanda sun je wurin da lamarin ya faru inda suka sami marigayin a kwance jina-jina, suka kai Babban Asibitin Giaɗe kuma likitan ya tabbatar da cewa ya rasu. An kuma miƙa gawarsa ga iyalansa domin yin jana’izarsa kamar yadda shari’ar Musulunci ta tanada.”

Ya ci gaba da cewa rundunar tana ci gaba da gudanar da bincike, babban wanda ake zargin kuma yana hannun ’yan sanda kuma bayan an kammala bincike za a gurfanar da shi a gaban kotu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Giaɗe

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano

Rundunar ’yan sandan Jihar Katsina ta kama gungun mutane 11 da ake zargi da kasancewa ’yan fashi da makami da ke addabar matafiya a kan hanyar Katsina zuwa Kano.

Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, Abubakar Aliyu, ya shaida wa manema labarai a ranar Laraba a Katsina cewa waɗanda ake zargin sun kware wajen tare hanyoyin zuwa Sha’iskawa-Charanchi da Katsina-Kankia-Kano, suna kwace dukiyoyin matafiya.

DSS ta cafke tsoffin jami’anta 2 kan aikata zamba Kotu ta daure kocin kwallon kafa a Kano shekara 8 saboda aikata luwadi

Ya bayyana sunayen waɗanda aka kama da suka haɗa da Dikko Ma’aru, Dardau Kabir, Muntari Musa, Labaran Amadu, Usman Ma’aru, Lawal Zubairu, Nasiru Sanusi, da Adamu Kabir.

Sauran sun haɗa da Abdullahi Zubairu, Muhammad Usman da Sale Shehu, dukkaninsu ’yan tsakanin shekaru 21 zuwa 35.

Ya ce, “Nasarar ta samu ne a ranar Lahadi da misalin ƙarfe 10 na safe lokacin da aka cafke ɗaya daga cikin gungun yayin da yake ƙoƙarin sayar da wasu kayayyakin da suka yi fashin su, bayan samun sahihin bayanan sirri.

“Bayan samun wannan bayani, jami’anmu sun bi sahu suka kama wanda ake zargin, lamarin da ya kai ga kama sauran ’yan gungun,” in ji shi.

Kakakin ’yan sandan ya ce yayin bincike, an samu agogo guda 80, wayoyi 9 da wuka daga hannun waɗanda ake zargin a matsayin shaidu.

Ya ƙara da cewa Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Bello Shehu, ya yaba da ƙoƙarin jami’an da suka gudanar da aikin, tare da nuna godiya ga goyon bayan jama’a.

Aliyu ya rawaito Kwamishinan yana ƙara kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da muhimman bayanai da za su taimaka wajen yaƙi da laifuka a jihar.

Ya kuma ce za a gurfanar da waɗanda ake zargin a gaban kotu da zarar an kammala bincike.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun kama gungun masu fashi a kan hanyar Katsina zuwa Kano
  • An Kashe Mutum 13 A Wasu Sabbin Hare-Hare A Ƙauyukan Filato
  • An kama mutum shida yayin da ‘yan sanda suka kubutar da mutane uku da aka yi garkuwa da su a Bauchi.
  • Kotu ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Kotun ta umarci a tono gawarwakin wadanda gobara ta kashe a Legas don yin bincike
  • Gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi Ta Tura Ɗalibai 117 Karatu Ƙasar Algeria 
  • An Kashe Mutum 3, Wasu 7 Sun Jikkata Sakamakon Ɓarkewar Rikici A Jihar Jigawa
  • Sakin Maryam Sanda shi ne ƙololuwar zalunci —Dangin Bilyaminu
  • ‘Yan Sandan Jihar Neja Sun Tabbatar Da Masu Sa-kai Kan Sahihiyar Kariya.
  • Hukumar Hisbah Ta Kama Wasu Matasa Da Suka Yi Aure Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Kano